< Matthew 3 >

1 And in those days cometh John the Baptist, proclaiming in the wilderness of Judea,
A kwanakin nan Yahaya Mai baftisma ya zo, yana wa'azi a jejin Yahudiya yana cewa,
2 and saying, 'Reform, for come nigh hath the reign of the heavens,'
“Ku tuba, domin mulkin sama ya kusa.”
3 for this is he who was spoken of by Isaiah the prophet, saying, 'A voice of one crying in the wilderness, Prepare ye the way of the Lord, straight make ye His paths.'
Wannan shine wanda annabi Ishaya ya yi maganarsa, ya ce, “Muryar wani mai kira a jeji yana cewa, 'Ku shirya wa Ubangiji hanyarsa, ku daidaita tafarkunsa.''
4 And this John had his clothing of camel's hair, and a girdle of skin round his loins, and his nourishment was locusts and honey of the field.
Yahaya kuwa yana sanye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma daure da damarar fata, abincinsa kuwa fara ne da zuman jeji.
5 Then were going forth unto him Jerusalem, and all Judea, and all the region round about the Jordan,
Sai mutanen Urushalima, da na dukan Yahudiya, da na duk kasashen bakin Kogin Urdun, suka yi ta zuwa wurin sa.
6 and they were baptized in the Jordan by him, confessing their sins.
Ya yi masu baftisma a Kogin Urdun, yayinda suke furta zunubansu.
7 And having seen many of the Pharisees and Sadducees coming about his baptism, he said to them, 'Brood of vipers! who did shew you to flee from the coming wrath?
Amma da ya ga Farisawa da Sadukiyawa da yawa, suna fitowa domin a yi masu baftisma, sai ya ce masu, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargade ku ku guje wa fushi mai zuwa?
8 bear, therefore, fruits worthy of the reformation,
Ku ba da 'ya'ya da za su nuna tubanku.
9 and do not think to say in yourselves, A father we have — Abraham, for I say to you, that God is able out of these stones to raise children to Abraham,
Kada kuwa ku dauka a ranku cewa, 'Ibrahim ne ubanmu.' Domin ina gaya maku, Allah yana da iko ya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin duwatsun nan.
10 and now also, the axe unto the root of the trees is laid, every tree therefore not bearing good fruit is hewn down, and to fire is cast.
Ko yanzu ma an sa gatari a gindin bishiyoyin. Saboda haka duk bishiyar da ba ta ba da 'ya'ya masu kyau ba, sai a sare ta a jefa a wuta.
11 'I indeed do baptize you with water to reformation, but he who after me is coming is mightier than I, of whom I am not worthy to bear the sandals, he shall baptize you with the Holy Spirit and with fire,
Na yi maku baftisma da ruwa, zuwa tuba. Amma mai zuwa baya na, ya fi ni girma, wanda ko takalmansa ma ban isa in dauka ba. Shi ne zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki, da kuma wuta.
12 whose fan [is] in his hand, and he will thoroughly cleanse his floor, and will gather his wheat to the storehouse, but the chaff he will burn with fire unquenchable.'
Kwaryar shikarsa na hannunsa, zai kuwa share masussukarsa sarai, ya tara alkamarsa ya sa a rumbunsa, amma zai kona buntun da wutar da ba za a iya kashewa ba.”
13 Then cometh Jesus from Galilee upon the Jordan, unto John to be baptized by him,
Sai Yesu ya zo daga kasar Galili, ya je Kogin Urdun wurin Yahaya, domin ya yi masa baftisma.
14 but John was forbidding him, saying, 'I have need by thee to be baptized — and thou dost come unto me!'
Amma Yahaya ya yi ta kokarin ya hana shi, yana cewa, “Ni da nake bukatar ka yi mani baftisma, ka zo gare ni?”
15 But Jesus answering said to him, 'Suffer now, for thus it is becoming to us to fulfil all righteousness,' then he doth suffer him.
Yesu ya amsa masa ya ce, “Bari ya zama haka a yanzu, domin a cika dukan adalci.” Sai Yahaya ya yarje masa.
16 And having been baptized, Jesus went up immediately from the water, and lo, opened to him were the heavens, and he saw the Spirit of God descending as a dove, and coming upon him,
Bayan da aka yi masa baftisma, Yesu ya fito nan da nan daga cikin ruwan, sai kuma sammai suka bude masa. Ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya, ya sauko a kansa.
17 and lo, a voice out of the heavens, saying, 'This is My Son — the Beloved, in whom I did delight.'
Duba, wata murya daga sammai tana cewa, ''Wannan shi ne kaunataccen Da na. Wanda ya gamshe ni sosai.''

< Matthew 3 >