< Matthew 12 >
1 At that time did Jesus go on the sabbaths through the corn, and his disciples were hungry, and they began to pluck ears, and to eat,
A wannan lokaci, Yesu ya tafi a ranar Asabaci, ya bi cikin gonar hatsi. Almajiransa na jin yunwa, sai suka fara zagar hatsi suna ci.
2 and the Pharisees having seen, said to him, 'Lo, thy disciples do that which it is not lawful to do on a sabbath.'
Amma da Farisawa suka gan su, sai su ka ce wa Yesu. “Duba, almajiranka su na yin abin da doka ta haramta a ranar Asabaci.”
3 And he said to them, 'Did ye not read what David did, when he was hungry, himself and those with him —
Amma Yesu ya ce masu, “Baku karanta abin da Dauda ya yi ba, lokacin da ya ke jin yunwa, tare da mazan da ke tare da shi?
4 how he went into the house of God, and the loaves of the presentation did eat, which it is not lawful to him to eat, nor to those with him, except to the priests alone?
Yadda ya shiga gidan Allah, ya ci gurasar alfarwa da doka ta hana shi ko mazan da ke tare da shi su ci, sai dai Firistoci ne kawai doka ta basu damar ci?
5 'Or did ye not read in the Law, that on the sabbaths the priests in the temple do profane the sabbath, and are blameless?
Sa'annan ba ku karanta cikin shari'a cewa, a ranar Asabaci, Firistoci da ke cikin haikali na sabawa ranar Asabaci, amma kamar ba su yi laifi ba?
6 and I say to you, that a greater than the temple is here;
Amma ina tabbatar maku da cewa, wani wanda ya fi haikali girma yana nan.
7 and if ye had known what is: Kindness I will, and not sacrifice — ye had not condemned the blameless,
In da kun san ma'anar wannan 'Na fi son jinkai fiye da hadaya,' da baku shari'anta wa marar laifi ba.
8 for the son of man is lord even of the sabbath.'
Gama Dan mutum shine Ubangijin Asabaci.”
9 And having departed thence, he went to their synagogue,
Sa'annan Yesu ya bar wannan wuri, ya shiga majami'ar su.
10 and lo, there was a man having the hand withered, and they questioned him, saying, 'Is it lawful to heal on the sabbaths?' that they might accuse him.
Sai ga wani mutum wanda hannun sa ya shanye, sai Farisawa suka tambayi Yesu, cewa, “Doka ta halarta a yi warkarwa a ranar Asabaci?” Domin su zarge shi a kan zunubi.
11 And he said to them, 'What man shall be of you, who shall have one sheep, and if this may fall on the sabbaths into a ditch, will not lay hold on it and raise [it]?
Yesu ya ce masu, “Wanene a cikin ku, wanda idan ya na da tunkiya guda, sa'annan tunkiyar nan ta fada a rami mai zurfi a ranar Asabaci ba zai kamo ta ya fitar da ita ba?
12 How much better, therefore, is a man than a sheep? — so that it is lawful on the sabbaths to do good.'
Yaya za a kwatanta darajar mutum da tunkiya! Saboda haka ya halarta a yi alheri ranar Asabaci.”
13 Then saith he to the man, 'Stretch forth thy hand,' and he stretched [it] forth, and it was restored whole as the other.
Sai Yesu ya ce wa mutumin nan “Mika hannun ka.” Ya mike hannunsa, sai hannun nan ya dawo lafiyaye kamar dayan hannunsa.
14 And the Pharisees having gone forth, held a consultation against him, how they might destroy him,
Amma Farisawa su ka fita waje su ka fara mugun shiri domin sa. Su na neman hanyar da za su kashe shi.
15 and Jesus having known, withdrew thence, and there followed him great multitudes, and he healed them all,
Da Yesu ya fahimci wannan, sai ya janye kan sa daga nan. Mutane da dama su ka bi shi, ya warkar da su duka.
16 and did charge them that they might not make him manifest,
Ya dokace su da kada su bayyana shi ga kowa,
17 that it might be fulfilled that was spoken through Isaiah the prophet, saying,
domin ya zama gaskiyar abin da aka fada ta wurin annabi Ishaya, cewa,
18 'Lo, My servant, whom I did choose, My beloved, in whom My soul did delight, I will put My Spirit upon him, and judgment to the nations he shall declare,
“Dubi, bawa na zababbe; kaunatacce na, wanda ya ke faranta mani raina sosai. Zan sa Ruhu na bisan sa, za ya furta hukunci zuwa al'ummai.
19 he shall not strive nor cry, nor shall any hear in the broad places his voice,
Ba za ya yi jayayya ko tada murya ba, babu wanda za ya ji muryar sa a karabku.
20 a bruised reed he shall not break, and smoking flax he shall not quench, till he may put forth judgment to victory,
Ba zai karya kara da ya tankwashe ba; ba zai kashe fitilar da ta kusa mutuwa ba; sai ya kawo hukunci ga nasara.
21 and in his name shall nations hope.'
Sa'annan al'ummai za su dogara a ga sunansa.
22 Then was brought to him a demoniac, blind and dumb, and he healed him, so that the blind and dumb both spake and saw.
Sa'annan wani mutum, makaho ne, kurma kuma, aljannu kuma na cikinsa, an kawo shi wurin Yesu. Ya warkar da shi, ya sami ganin gari ya kuma yi magana.
23 And all the multitudes were amazed, and said, 'Is this the Son of David?'
Jama'a su ka yi mamaki kwarai, su na cewa, “Ko wannan ne Dan Dawuda?”
24 but the Pharisees having heard, said, 'This one doth not cast out demons, except by Beelzeboul, ruler of the demons.'
Amma da Farisawa su ka ji wannan al'ajibi, sai su ka ce, “Mutumin nan yana fitar da aljannu ta wurin Bahalzabuba sarkin aljannu ne.”
25 And Jesus, knowing their thoughts, said to them, 'Every kingdom having been divided against itself is desolated, and no city or house having been divided against itself, doth stand,
Amma Yesu ya san tunanin su, sai ya ce. “Duk mulkin da ya rabu gaba da kan sa, ba zaya tsaya ba, duk wani birni da ya rabu ba zai tsaya ba, ko gida da ya tsage, za ya rushe.
26 and if the Adversary doth cast out the Adversary, against himself he was divided, how then doth his kingdom stand?
Idan Shaidan ya fitar da Shaidan, ya rabu gaba da kansa. Yaya mulkin sa za ya tsaya?
27 'And if I, by Beelzeboul, do cast out the demons, your sons — by whom do they cast out? because of this they — they shall be your judges.
Idan Ina fitar da aljannu da ikon Ba'alzabuba, ta wurin wa masu bin ku su ke fitar da su? Saboda haka, su za su shari'anta ku.
28 'But if I, by the Spirit of God, do cast out the demons, then come already unto you did the reign of God.
Amma idan ina fitar da aljannu da Ruhun Allah ne, hakika mulkin Allah ya zo gare ku.
29 'Or how is one able to go into the house of the strong man, and to plunder his goods, if first he may not bind the strong man? and then his house he will plunder.
Kuma ta yaya mutum za ya shiga gidan mai karfi ya kwashe masa kaya ba tare da ya fara daure shi ba? Sa'annan ne za ya iya satar masa kaya daga gidansa.
30 'He who is not with me is against me, and he who is not gathering with me, doth scatter.
Wanda baya tare da ni yana gaba da ni ke nan, wanda kuma baya tarawa tare da ni, yana watsarwa ne.
31 Because of this I say to you, all sin and evil speaking shall be forgiven to men, but the evil speaking of the Spirit shall not be forgiven to men.
Saboda haka ina ce maku, kowanne zunubi da sabo, za a gafarta wa mutum, amma sabon Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta shi ba.
32 And whoever may speak a word against the Son of Man it shall be forgiven to him, but whoever may speak against the Holy Spirit, it shall not be forgiven him, neither in this age, nor in that which is coming. (aiōn )
Duk wanda yayi batanci ga Dan Mutum, za a gafarta masa. Amma duk wanda yayi batanci game da Ruhu Mai Tsarki ba za a gafarta masa ba, a nan duniya da har abada. (aiōn )
33 'Either make the tree good, and its fruit good, or make the tree bad, and its fruit bad, for from the fruit is the tree known.
Ko dai a mai da itace mai kyau 'ya'yansa kuma su yi kyau, ko a mai da itace marar kyau 'ya'yansa kuma marasa kyau, gama ana sanin itace ta wurin 'ya'yansa.
34 'Brood of vipers! how are ye able to speak good things — being evil? for out of the abundance of the heart doth the mouth speak.
Ku 'ya'yan macizai, tun da ku miyagu ne, yaya za ku iya fadin abubuwa nagari? Gama daga cikar zuciya baki ke magana.
35 The good man out of the good treasure of the heart doth put forth the good things, and the evil man out of the evil treasure doth put forth evil things.
Mutumin kirki daga ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwa masu kyau, mugun mutum kuma daga mummunar ajiyar zuciyarsa ya kan fitar da abubuwan mugunta.
36 'And I say to you, that every idle word that men may speak, they shall give for it a reckoning in a day of judgment;
Sa'annan ina ce maku a ranar shari'a, mutane za su bada lissafin abubuwan banza da su ka fadi.
37 for from thy words thou shalt be declared righteous, and from thy words thou shalt be declared unrighteous.'
Gama ta wurin maganganun ku, za a 'yantar da ku, ta wurin maganganun ku kuma za a kashe ku.”
38 Then answered certain of the scribes and Pharisees, saying, 'Teacher, we will to see a sign from thee.'
Sa'annan wadansu Malaman Attaura, da Farisawa suka amsa suka ce wa Yesu, “Mallam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.”
39 And he answering said to them, 'A generation, evil and adulterous, doth seek a sign, and a sign shall not be given to it, except the sign of Jonah the prophet;
Amma Yesu ya amsa ya ce masu, “Mugun zamani da mazinaciyar tsara, su na bukutar alama. Amma babu alamar da za a ba su, sai dai alamar annabi Yunusa.
40 for, as Jonah was in the belly of the fish three days and three nights, so shall the Son of Man be in the heart of the earth three days and three nights.
Gama yadda Yunusa ya yi kwana uku da dare uku a cikin babban kifi, haka ma Dan Mutum zaya yi kwana uku da dare uku a cikin zuciyar kasa.
41 'Men of Nineveh shall stand up in the judgment with this generation, and shall condemn it, for they reformed at the proclamation of Jonah, and lo, a greater than Jonah here!
Mutanen Nineba za su tsaya a ranar shari'a da wannan zamani sannan su kashe su. Domin sun tuba da suka ji wa'azin Yunusa, amma duba wanda ya fi Yunusa yana nan.
42 'A queen of the south shall rise up in the judgment with this generation, and shall condemn it, for she came from the ends of the earth to hear the wisdom of Solomon, and lo, a greater than Solomon here!
Sarauniyar Kudu za ta tashi da mutanen wannan zamani ta kuma kashe su. Ta zo daga karshen duniya domin ta ji hikimar Sulaimanu, kuma duba, wanda ya fi Sulaimanu yana nan.
43 'And, when the unclean spirit may go forth from the man, it doth walk through dry places seeking rest, and doth not find;
Idan kazamin ruhu ya rabu da mutum, ya kan wuce ya nemi wuraren da ruwa yake domin ya huta, amma bai samu ba.
44 then it saith, I will turn back to my house whence I came forth; and having come, it findeth [it] unoccupied, swept, and adorned:
Sai ya ce, 'zan koma gidana inda na fito'. Bayan ya dawo, sai ya tarar da gidan nan an share shi ya zama da tsabta.
45 then doth it go, and take with itself seven other spirits more evil than itself, and having gone in they dwell there, and the last of that man doth become worse than the first; so shall it be also to this evil generation.'
Sai ya koma ya kawo wadansu ruhohi guda bakwai, wadanda su ka fi shi mugunta, sa'annan dukan su su zo su zauna a nan. Sa'annan yanayin mutumin nan na karshe ya fi na farko muni. Haka zaya kasance ga wannan mugun zamani.
46 And while he was yet speaking to the multitudes, lo, his mother and brethren had stood without, seeking to speak to him,
Sa'adda Yesu ya ke yi wa Jama'a jawabi, sai mahaifiyarsa da 'yan'uwansa su ka zo su ka tsaya a waje, suna neman su yi magana da shi.
47 and one said to him, 'Lo, thy mother and thy brethren do stand without, seeking to speak to thee.'
Sai wani ya ce masa, “Duba, mahaifiyarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai”.
48 And he answering said to him who spake to him, 'Who is my mother? and who are my brethren?'
Amma Yesu ya amsa ya ce wa shi wanda ya gaya masa, “Wacece mahaifiyata? Kuma su wanene 'yan'uwana?”
49 And having stretched forth his hand toward his disciples, he said, 'Lo, my mother and my brethren!
Sai ya mika hannu ya nuna almajiransa ya ce, “Duba, ga mahaifiyata da 'yan'uwana!
50 for whoever may do the will of my Father who is in the heavens, he is my brother, and sister, and mother.'
Gama duk wanda yake aikata nufin Ubana wanda ya ke cikin sama, shine dan'uwana, da 'yar'uwata da mahaifiyata.”