< Mark 6 >

1 And he went forth thence, and came to his own country, and his disciples do follow him,
Ya bar su ya zo garinsu, almajiransa su ka biyo shi.
2 and sabbath having come, he began in the synagogue to teach, and many hearing were astonished, saying, 'Whence hath this one these things? and what the wisdom that was given to him, that also such mighty works through his hands are done?
Sa'adda ranar Asabar tazo ya shiga cikin masujada ya yi koyarwa. Mutane da yawa da su ka ji koyarwarsa su ka yi mamaki, suka ce daga ina ya sami irin wannan koyarwar? Wacce irin hikima ce Allah ya ba shi haka? Wadanne irin ayyukan al'ajibi ya ke yi da hannuwansa?
3 Is not this the carpenter, the son of Mary, and brother of James, and Joses, and Judas, and Simon? and are not his sisters here with us?' — and they were being stumbled at him.
Wannan ba kafintan nan ba ne dan Maryamu, dan'uwan Yakubu da Yosi da Yahuza da Saminu? Ba ga 'yan'uwan sa 'yan mata mu na tare da su ba? Ba su ji dadi ba a ransu saboda Yesu.
4 And Jesus said to them — 'A prophet is not without honour, except in his own country, and among his kindred, and in his own house;'
Yesu ya ce, “Annabi ba ya rasa daraja sai a gidansa da garinsa da cikin danginsa.”
5 and he was not able there any mighty work to do, except on a few infirm people having put hands he did heal [them];
Bai iya yin wani aikin al'ajibi a wurin ba sai dai mutane kadan marasa lafiya ya dorawa hannu ya warkar da su.
6 and he wondered because of their unbelief. And he was going round the villages, in a circle, teaching,
Rashin bangaskiyarsu ya ba shi mamaki. Sai ya tafi cikin kauyuka na kewaye da su ya yi ta koyarwa.
7 and he doth call near the twelve, and he began to send them forth two by two, and he was giving them power over the unclean spirits,
Ya kira almajiransa su goma sha biyu, ya aike su biyu-biyu, ya ba su iko a kan aljanu,
8 and he commanded them that they may take nothing for the way, except a staff only — no scrip, no bread, no brass in the girdle,
ya dokace su kada su dauki komai tare da su domin wannan tafiya, sai dai sanda kadai. Kada su dauki abinci ko jaka ko kudi a cikin aljihunsu,
9 but having been shod with sandals, and ye may not put on two coats.
sai dai su sa takalmi kadai, kada su sa taguwa biyu a jikinsu.
10 And he said to them, 'Whenever ye may enter into a house, there remain till ye may depart thence,
Ya ce da su, idan ku ka shiga wani gida sai ku zauna a gidan har lokacin da za ku tashi.
11 and as many as may not receive you, nor hear you, going out thence, shake off the dust that is under your feet for a testimony to them; verily I say to you, It shall be more tolerable for Sodom or Gomorrah in a day of judgment than for that city.'
Idan ku ka je wani gari aka ki karbar ku, ku karkabe kurar da ke kafufunku ta zama shaida kan mutanen garin.
12 And having gone forth they were preaching that [men] might reform,
Sai suka tafi suka yi ta shela ga mutane cewa su tuba daga zunubansu.
13 and many demons they were casting out, and they were anointing with oil many infirm, and they were healing [them].
Sun fitar da aljanu da yawa, suka shafawa mutane da yawa mai suka warkar da su.
14 And the king Herod heard, (for his name became public, ) and he said — 'John the Baptist out of the dead was raised, and because of this the mighty powers are working in him.'
Sarki Hirudus ya ji wannan, gama sunan Yesu ya zama sananne a wurin kowa da kowa. Wadansu suna cewa Yahaya mai yin baftisma ne ya tashi daga matattu shi ya sa ake yin wadannan ayyukan al'ajibi ta wurinsa.
15 Others said — 'It is Elijah,' and others said — 'It is a prophet, or as one of the prophets.'
Wadansu kuma suna cewa, “Iliya,” Har yanzu wadansu suna cewa daya “daga cikin annabawa ne na da can.”
16 And Herod having heard, said — 'He whom I did behead — John — this is he; he was raised out of the dead.'
Sa'adda Hirudus ya ji wannan sai ya ce, “Yahaya wanda na fillewa kai shine ya tashi.”
17 For Herod himself, having sent forth, did lay hold on John, and bound him in the prison, because of Herodias the wife of Philip his brother, because he married her,
Saboda Hirudus ne ya sa aka kama Yahaya aka kulle shi a kurkuku saboda Hirodiya( matar Filibus dan'uwansa), domin ya aure ta.
18 for John said to Herod — 'It is not lawful to thee to have the wife of thy brother;'
Saboda Yahaya ya gaya wa Hirudus cewa bai halarta ya auri matar dan'uwansa ba.
19 and Herodias was having a quarrel with him, and was willing to kill him, and was not able,
Sai ita Hirodiya ta yi kudurin ta kashe Yahaya amma bai yiwu ba.
20 for Herod was fearing John, knowing him a man righteous and holy, and was keeping watch over him, and having heard him, was doing many things, and hearing him gladly.
Domin Hirudus yana jin tsoron Yahaya, domin ya sani shi mai adalci ce, mai tsarki kuma. Domin haka Hirudus bai so wani abu ya faru da Yahaya ba, amma ya kan fusata idan ya ji wa'azin yahaya. Duk da haka da fari ciki yakan saurare shi.
21 And a seasonable day having come, when Herod on his birthday was making a supper to his great men, and to the chiefs of thousands, and to the first men of Galilee,
Amma sai dama ta samu inda Hirodiya za ta iya yin abin da ta ke so ta yi. A lokacin kewayowar ranar haihuwar sa, sai Hirudus ya shirya liyafa domin manyan da ke aiki tare da shi a cikin gwamnatin sa, da shugabannin da ke cikin Galili.
22 and the daughter of that Herodias having come in, and having danced, and having pleased Herod and those reclining (at meat) with him, the king said to the damsel, 'Ask of me whatever thou wilt, and I will give to thee,'
Diyar Hirodiya ta zo ta yi masu rawa, rawarta kuwa tagamshi Hirudus da bakinsa. Sarki ya ce da yarinyar, “ki tambayi duk abin da ki ke so ni kuwa zan ba ki shi”.
23 and he sware to her — 'Whatever thou mayest ask me, I will give to thee — unto the half of my kingdom.'
Ya rantse mata da cewa”Ko menene ki ka ce ki na so, ko da rabin mulkina ne”
24 And she, having gone forth, said to her mother, 'What shall I ask for myself?' and she said, 'The head of John the Baptist;'
Sai ta fita ta je ta tambayi mamarta, “me zan ce ya bani?” Sai ta ce kan Yahaya Mai Yin Baftisma.
25 and having come in immediately with haste unto the king, she asked, saying, 'I will that thou mayest give me presently, upon a plate, the head of John the Baptist.'
Sai ta dawo da sauri cikin dakin taro wurin sarki ta ce da shi, “Ina so ka ba ni kan Yahaya Mai Yin Baftisma a cikin tire.”
26 And the king — made very sorrowful — because of the oaths and of those reclining (at meat) with him, would not put her away,
Sarki ya damu kwarai, amma saboda ya yi alkawari ga kuma ofisoshinsa, ba dama ya ce a'a.
27 and immediately the king having sent a guardsman, did command his head to be brought,
Sai sarki ya aiki wani soja ya ba shi ummurni ya je ya kawo kan Yahaya. Sojan ya je ya fillo kan sa daga cikin kurkuku.
28 and he having gone, beheaded him in the prison, and brought his head upon a plate, and did give it to the damsel, and the damsel did give it to her mother;
Ya kawo kan a cikin tire ya ba yarinyar, yarinyar kuma ta kai wa mamarta.
29 and having heard, his disciples came and took up his corpse, and laid it in the tomb.
Da almajiran su ka ji labari, suka zo suka dauki gawarsa suka rufe a cikin kabari.
30 And the apostles are gathered together unto Jesus, and they told him all, and how many things they did, and how many things they taught,
Almajiran suka zo wurin Yesu, suka fada masa dukkan abin da suka yi da abin da suka koyar.
31 and he said to them, 'Come ye yourselves apart to a desert place, and rest a little,' for those coming and those going were many, and not even to eat had they opportunity,
Sai ya ce da su “ku je cikin kebabben wuri domin ku huta kadan,” domin mutane suna ta kaiwa da komowa, ba su sami damar hutawa ba balle su ci abinci
32 and they went away to a desert place, in the boat, by themselves.
Sai suka tafi kebabben wuri a cikin jirgin ruwa su kadai.
33 And the multitudes saw them going away, and many recognised him, and by land from all the cities they ran thither, and went before them, and came together to him,
Amma mutane da yawa sun gansu suna tafiya sun kuma gane su, sai suka fito daga cikin dukan garuruwa da gudu har su ka kai wurin kafin su zo.
34 and having come forth, Jesus saw a great multitude, and was moved with compassion on them, that they were as sheep not having a shepherd, and he began to teach many things.
Sa'adda suka zo bakin gaba Yesu ya ga taron mutane da yawa sai ya ji tausayinsu domin sun yi kamar tumakin da ba da mai kiwo. Sai ya cigaba da koya masu abubuwa da yawa.
35 And now the hour being advanced, his disciples having come near to him, say, — 'The place is desolate, and the hour is now advanced,
Sa'adda yamma ta yi, almajiran sa suka zo suka ce da shi, “wurinnan kebabben wuri ne kuma ga lokaci ya tafi.
36 let them away, that, having gone away to the surrounding fields and villages, they may buy to themselves loaves, for what they may eat they have not.'
Ka sallami mutanen nan domin su shiga cikin garuruwa da kauyuka da ke kusa domin su sayi abin da zasu ci.
37 And he answering said to them, 'Give ye them to eat,' and they say to him, 'Having gone away, may we buy two hundred denaries' worth of loaves, and give to them to eat?'
Amma sai ya ba su amsa ya ce,”Ku ku basu abinci su ci mana”. Sai suka ce da shi, “ma iya zuwa mu sawo gurasa ta sule dari biyu mu basu su ci?”
38 And he saith to them, 'How many loaves have ye? go and see;' and having known, they say, 'Five, and two fishes.'
Sai ya ce dasu, “Dunkulen gurasa guda nawa kuke dasu? Kuje ku gani.” Dasuka gano sai suka ce da shi, dunkule biyar ne da kifi guda biyu.”
39 And he commanded them to make all recline in companies upon the green grass,
Sai ya ba da umarni mutanen su dukka su zauna a kan danyar ciyawa.
40 and they sat down in squares, by hundreds, and by fifties.
Suka zauna kungiya kungiya wadansu su dari wadansu hamsin.
41 And having taken the five loaves and the two fishes, having looked up to the heaven, he blessed, and brake the loaves, and was giving to his disciples, that they may set before them, and the two fishes divided he to all,
Sai ya dauki dunkulen gurasa guda biyar da kifi guda biyu, ya ta da kansa sama, yasa albarka, ya kakkarya dunkulen gurasan, ya ba almajiran domin su rabawa taron jama'a duka.
42 and they did all eat, and were filled,
Dukansu suka ci suka koshi.
43 and they took up of broken pieces twelve hand-baskets full, and of the fishes,
Suka tattara gutsattsarin gurasar suka cika kwanduna guda goma sha biyu da gutsattsarin da kuma gutsattsarin kifin.
44 and those eating of the loaves were about five thousand men.
Mutanen da suka ci gurasar sun kai mutum dubu biyar.
45 And immediately he constrained his disciples to go into the boat, and to go before to the other side, unto Bethsaida, till he may let the multitude away,
Nan da nan ya ce almajiran sa su hau jirgin ruwa su yi gaba kafin ya zo, su je Baitsaida. Shi kuma ya tsaya domin ya sallami taron mutanen.
46 and having taken leave of them, he went away to the mountain to pray.
Bayan da suka tafi shi kuma ya hau kan dutse domin ya yi addu'a.
47 And evening having come, the boat was in the midst of the sea, and he alone upon the land;
Har yamma ta yi jirgin ruwan ya na tsakiyar rafi shi kuma yana kan tudu shi kadai.
48 and he saw them harassed in the rowing, for the wind was against them, and about the fourth watch of the night he doth come to them walking on the sea, and wished to pass by them.
Ya gansu suna wahala gama iska ta hana su tafiya. Wajan karfe hudu na asuba sai ya tawo wurin su yana tafiya a kan ruwa, yana so ya wuce gaban su.
49 And they having seen him walking on the sea, thought [it] to be an apparition, and cried out,
Sa'adda suka gan shi ya na tafiya a kan ruwa suka yi tsammani fatalwa ce, suka yi ihu,
50 for they all saw him, and were troubled, and immediately he spake with them, and saith to them, 'Take courage, I am [he], be not afraid.'
gama su duka sun gan shi, tsoro ya kama su. Sai nan da nan ya yi magana dasu ya ce, “Ku karfafa ni ne! kada ku ji tsoro!''
51 And he went up unto them to the boat, and the wind lulled, and greatly out of measure were they amazed in themselves, and were wondering,
Ya shiga cikin jirgin ruwan tare dasu, sai iska ta dena bugawa. Sai suka yi mamaki kwarai.
52 for they understood not concerning the loaves, for their heart hath been hard.
Gama basu gane batun dunkulen ba. Maimakon haka, sai zukatansu suka taurare.
53 And having passed over, they came upon the land of Gennesaret, and drew to the shore,
Sa'adda suka haye su zo kasar Janisarita suka sa wa jirgin sarka.
54 and they having come forth out of the boat, immediately having recognised him,
Su na fitowa daga cikin jirgin kenan, mutane suka gane cewa Yesu ne.
55 having run about through all that region round about, they began upon the couches to carry about those ill, where they were hearing that he is,
Mutane suka ruga cikin yankin su, suka kawo marasa lafiya a bisa shinfidun su zuwa wurinsa, dukan inda suka ji yana zuwa.
56 and wherever he was going, to villages, or cities, or fields, in the market-places they were laying the infirm, and were calling upon him, that they may touch if it were but the fringe of his garment, and as many as were touching him were saved.
Ko ina ya shiga birni da kauye, ko a cikin kasar sukan kawo marasa lafiya a kasuwanni suna rokonsa su taba ko da habar rigarsa, dukan wadanda suka taba kuwa suka warke.

< Mark 6 >