< Luke 23 >
1 And having risen, the whole multitude of them did lead him to Pilate,
Sai duk taron suka tashi, suka kawo Yesu gaban Bilatus.
2 and began to accuse him, saying, 'This one we found perverting the nation, and forbidding to give tribute to Caesar, saying himself to be Christ a king.'
Suka fara saransa, cewa “Mun same wannan mutum yana ruda kasarmu, ya haramta a ba Kaisar haraji, yana kuma cewa shi da kansa ne Almasihu, sarki.”
3 And Pilate questioned him, saying, 'Thou art the king of the Jews?' and he answering him, said, 'Thou dost say [it].'
Bilatus ya tambaye shi, cewa “Shin kaine Sarkin Yahudawa?” Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Haka ka ce.”
4 And Pilate said unto the chief priests, and the multitude, 'I find no fault in this man;'
Sai Bilatus ya ce wa manyan firistocin da taro mai yawa, “Ban samu ko laifi daya game da wannan mutumin ba.”
5 and they were the more urgent, saying — 'He doth stir up the people, teaching throughout the whole of Judea — having begun from Galilee — unto this place.'
Amma suka yi ta cewa, “Yana ta da hankalin mutane da koyarwa a dukan Yahudiya, ya fara daga Galili har zuwa ga wannan wuri.”
6 And Pilate having heard of Galilee, questioned if the man is a Galilean,
Sa'adda Bilatus ya ji wannan, sai ya tambaya ko mutumin daga Galiline.
7 and having known that he is from the jurisdiction of Herod, he sent him back unto Herod, he being also in Jerusalem in those days.
Sa'adda ya gane cewa yana karkashin mulkin Hirudus, sai ya tura Yesu wurin Hirudus, wanda shi da kansa yana Urushalima a wadannan kwanakin.
8 And Herod having seen Jesus did rejoice exceedingly, for he was wishing for a long [time] to see him, because of hearing many things about him, and he was hoping some sign to see done by him,
Sa'adda Hirudus ya ga Yesu, sai ya cika da farin ciki sosai, saboda ya so ganinsa tunda dadewa. Tun can ya ji game da shi sai ya yi begen ganin wadansu al'ajibai da zai yi.
9 and was questioning him in many words, and he answered him nothing.
Hirudus ya tambaye Yesu cikin kalmomi masu yawa, amma Yesu bai amsa masa da komai ba.
10 And the chief priests and the scribes stood vehemently accusing him,
Sai manyan firistoci da marubuta suka tsaya, suna ta yi masa zargi mai zafi.
11 and Herod with his soldiers having set him at nought, and having mocked, having put around him gorgeous apparel, did send him back to Pilate,
Hirudus da sojojinsa suka zarge shi, suka kuma yi masa ba'a, suka sa masa tufafi masu kyau, sa'annan ya sake aika Yesu zuwa wurin Bilatus.
12 and both Pilate and Herod became friends on that day with one another, for they were before at enmity between themselves.
Sai Hirudus da Bilatus suka zama abokai a wannan rana (da ma su abokai gaba ne).
13 And Pilate having called together the chief priests, and the rulers, and the people,
Bilatus ya kira manyan firistoci tare da masu mulki da kuma taron jama'ar,
14 said unto them, 'Ye brought to me this man as perverting the people, and lo, I before you having examined, found in this man no fault in those things ye bring forward against him;
sai ya ce masu, “Kun kawo mani wannan mutum kamar wanda yake jagorar mutane ga munanan ayyuka, ku kuma gani, Ni, na tuhume shi a gabanku, ban sami ko kuskure daya daga mutumin nan game da abinda ku ke zarginsa da shi ba.
15 no, nor yet Herod, for I sent you back unto him, and lo, nothing worthy of death is having been done by him;
Babu, ko Hirudus ma, ya sake komar mana da shi, kun gani, babu wani abu wanda ya yi da ya cancanci mutuwa,
16 having chastised, therefore, I will release him,'
saboda haka zan yi masa horo sa'annan in sake shi.”
17 for it was necessary for him to release to them one at every feast,
[Ya zama dole Bilatus ya sakar wa Yahudawa wani daurarre guda daya lokacin idin.]
18 and they cried out — the whole multitude — saying, 'Away with this one, and release to us Barabbas,'
Amma dukansu suka yi ihu tare, cewa, “A tafi da wannan mutumin, sai a sako mana Barabbas!”
19 who had been, because of a certain sedition made in the city, and murder, cast into prison.
Barabbas mutum ne wanda aka sa a cikin kurkuku saboda wani tada hankali a cikin birni da kuma kisankai.
20 Pilate again then — wishing to release Jesus — called to them,
Bilatus ya sake yi masu magana, yana so ya saki Yesu.
21 but they were calling out, saying, 'Crucify, crucify him.'
Amma suka yi ihu, cewa, “A giciye shi, a giciye shi.”
22 And he a third time said unto them, 'Why, what evil did he? no cause of death did I find in him; having chastised him, then, I will release [him].'
Sai ya sake ce masu sau na uku, “Don me, wace magunta wannan mutum ya yi? Ban sami wani abu da ya isa sanadin mutuwa game da shi ba. Saboda haka bayan na hore shi, zan sake shi.”
23 And they were pressing with loud voices asking him to be crucified, and their voices, and those of the chief priests, were prevailing,
Amma suka nace da murya mai karfi, suna so a giciye shi, sai muryarsu ta rinjayi Bilatus.
24 and Pilate gave judgment for their request being done,
Sai Bilatus ya yarda ya yi masu bisa ga abin da suke so.
25 and he released him who because of sedition and murder hath been cast into the prison, whom they were asking, and Jesus he gave up to their will.
Ya sako masu wanda suka tambaya ya ba su wanda aka sa a kurkuku domin tada hankali da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu bisa nufinsu.
26 And as they led him away, having taken hold on Simon, a certain Cyrenian, coming from the field, they put on him the cross, to bear [it] behind Jesus.
Da suka tafi da shi, sai suka kama wani mai suna siman Bakurane, yana zuwa daga karkara, sai suka daura masa giciyen ya dauka, yana biye da Yesu.
27 And there was following him a great multitude of the people, and of women, who also were beating themselves and lamenting him,
Babban taron jama'a, da na mata da suke makoki da kuka dominsa, suna binsa.
28 and Jesus having turned unto them, said, 'Daughters of Jerusalem, weep not for me, but for yourselves weep ye, and for your children;
Amma da ya juya wurinsu, Yesu yace, “Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka domina, amma ku yi kuka domin kanku da 'ya'yanku.
29 for, lo, days do come, in which they shall say, Happy the barren, and wombs that did not bare, and paps that did not give suck;
Gama ku gani, kwanaki suna zuwa da za su ce, 'Albarka ta tabbata ga bakararru da wadanda basu taba haihuwa ba da kuma wadanda ba a taba shan mamansu ba.'
30 then they shall begin to say to the mountains, Fall on us, and to the hills, Cover us; —
Sa'annan za su fara ce wa duwatsu, 'Ku fado bisanmu,' da tuddai ma, 'Ku rufe mu.'
31 for, if in the green tree they do these things — in the dry what may happen?'
Gama idan sun yi wadannan abubuwan lokacin da itace yana danye, me zai faru sa'adda ya bushe?”
32 And there were also others — two evil-doers — with him, to be put to death;
Aka kai wadansu mutum biyu masu laifi, domin a kashe shi tare da su.
33 and when they came to the place that is called Skull, there they crucified him and the evil-doers, one on the right hand and one on the left.
Sa'adda suka zo wurin da a ke kira kwalluwa, nan suka giciye shi da barayin, daya daga hannun damansa dayan kuma daga hannun hagu.
34 And Jesus said, 'Father, forgive them, for they have not known what they do;' and parting his garments they cast a lot.
Yesu yace, “Uba, ka yafe masu, gama basu san abin da suke yi ba.” Sai suka jefa kuri'a, suka rarraba tufafinsa.
35 And the people were standing, looking on, and the rulers also were sneering with them, saying, 'Others he saved, let him save himself, if this be the Christ, the choice one of God.'
Mutane sun tsaya suna kallo sa'annan masu mulki suna ta yin masa ba'a, cewa, “Ya ceci wadansu. Bari ya ceci kansa, idan shine Almasihu na Allah, zababben nan.”
36 And mocking him also were the soldiers, coming near and offering vinegar to him,
Sojojin ma suka yi masa dariya, suna zuwa wurinsa, suna mika masa ruwan tsami,
37 and saying, 'If thou be the king of the Jews, save thyself.'
suna cewa, “Idan kai Sarkin Yahudawa ne, ceci kanka.”
38 And there was also a superscription written over him, in letters of Greek, and Roman, and Hebrew, 'This is the King of the Jews.'
Akwai wata alama bisansa, “Wannan shine Sarkin Yahudawa.”
39 And one of the evil-doers who were hanged, was speaking evil of him, saying, 'If thou be the Christ, save thyself and us.'
Daya daga cikin barayi wanda aka giciye, ya zage shi, cewa, “Ba kai ne Almasihu ba? Ka ceci kanka da mu.”
40 And the other answering, was rebuking him, saying, 'Dost thou not even fear God, that thou art in the same judgment?
Amma dayan ya amsa, ya tsauta masa cewa, “Ba ka tsoron Allah, da yake shari'arka daya ne da nasa?
41 and we indeed righteously, for things worthy of what we did we receive back, but this one did nothing out of place;'
Mu kam an yi ma na daidai, gama mun samu bisa ga abin da muka yi. Amma wannan mutum bai yi wani abu mara kyau ba.”
42 and he said to Jesus, 'Remember me, lord, when thou mayest come in thy reign;'
Sai ya kara, “Yesu, ka tuna da ni sa'adda ka shiga mulkinka.”
43 and Jesus said to him, 'Verily I say to thee, To-day with me thou shalt be in the paradise.'
Yesu ya ce masa, “Gaskiya ina ce maka, yau za ka kasance tare da ni a firdausi.”
44 And it was, as it were, the sixth hour, and darkness came over all the land till the ninth hour,
Anan nan a wajen sa'a na shida, sai duhu ya mamaye kasar duka har zuwa sa'a na tara
45 and the sun was darkened, and the vail of the sanctuary was rent in the midst,
sa'adda rana ya fadi. Sai labulen haikalin ya rabu a tsakiya zuwa kasa.
46 and having cried with a loud voice, Jesus said, 'Father, to Thy hands I commit my spirit;' and these things having said, he breathed forth the spirit.
Da kuka da murya mai karfi, Yesu yace, “Uba, na mika Ruhu na a hannunka.” Bayan da ya fadi wannan, sai ya mutu.
47 And the centurion having seen what was done, did glorify God, saying, 'Really this man was righteous;'
Sa'adda jarumin ya ga abin da ya faru, ya daukaka Allah, cewa, “Lallai wannan mutumin mai adalci ne.”
48 and all the multitudes who were come together to this sight, beholding the things that came to pass, smiting their breasts did turn back;
Sa'adda dukan taro mai yawa wadanda suka zo tare domin su shaida da idanunsu suka ga abubuwan da suka faru, suka koma suna bugan kirjinsu.
49 and all his acquaintances stood afar off, and women who did follow him from Galilee, beholding these things.
Amma duk idon sani, da kuma matan da suka bi shi tun daga Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban wadannan abubuwa.
50 And lo, a man, by name Joseph, being a counsellor, a man good and righteous,
Ga shi kuwa, wani mutum mai suna Yusufu, shi dan majalisa ne, nagari ne kuma mutum mai adalci ne
51 — he was not consenting to their counsel and deed — from Arimathea, a city of the Jews, who also himself was expecting the reign of God,
(bai yarda da shawarar da kuma abin da suka aikata ba), daga Arimatiya a kasar Yahudiya, wanda yake jiran mulkin Allah.
52 he, having gone near to Pilate, asked the body of Jesus,
Wannan mutum, ya sami Bilatus, ya tambaya a bashi jikin Yesu.
53 and having taken it down, he wrapped it in fine linen, and placed it in a tomb hewn out, where no one was yet laid.
Ya saukar da shi kasa, sai ya nade shi cikin likafani na linin mai kyau, ya kwantar da shi cikin kabari da aka sassaka shi daga dutse, inda ba a taba binne wani ba.
54 And the day was a preparation, and sabbath was approaching,
Ranar kuwa, ranar shiri ce, Asabaci kuma ta kusato.
55 and the women also who have come with him out of Galilee having followed after, beheld the tomb, and how his body was placed,
Matan da suka taho da shi tun daga Galili, suka biyo baya, su ga kabarin da inda aka ajiye shi.
56 and having turned back, they made ready spices and ointments, and on the sabbath, indeed, they rested, according to the command.
Suka koma, sai suka shirya kayan kamshi da mai. Suka kuma huta a ranar Asabaci bisa ga doka.