< Luke 2 >

1 And it came to pass in those days, there went forth a decree from Caesar Augustus, that all the world be enrolled —
Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
2 this enrolment first came to pass when Cyrenius was governor of Syria —
Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
3 and all were going to be enrolled, each to his proper city,
Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
4 and Joseph also went up from Galilee, out of the city of Nazareth, to Judea, to the city of David, that is called Bethlehem, because of his being of the house and family of David,
Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
5 to enrol himself with Mary his betrothed wife, being with child.
Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
6 And it came to pass, in their being there, the days were fulfilled for her bringing forth,
Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
7 and she brought forth her son — the first-born, and wrapped him up, and laid him down in the manger, because there was not for them a place in the guest-chamber.
Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
8 And there were shepherds in the same region, lodging in the field, and keeping the night-watches over their flock,
A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
9 and lo, a messenger of the Lord stood over them, and the glory of the Lord shone around them, and they feared a great fear.
Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
10 And the messenger said to them, 'Fear not, for lo, I bring you good news of great joy, that shall be to all the people —
Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
11 because there was born to you to-day a Saviour — who is Christ the Lord — in the city of David,
Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
12 and this [is] to you the sign: Ye shall find a babe wrapped up, lying in the manger.'
Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
13 And suddenly there came with the messenger a multitude of the heavenly host, praising God, and saying,
Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
14 'Glory in the highest to God, and upon earth peace, among men — good will.'
“Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
15 And it came to pass, when the messengers were gone away from them to the heavens, that the men, the shepherds, said unto one another, 'We may go over indeed unto Bethlehem, and see this thing that hath come to pass, that the Lord did make known to us.'
Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
16 And they came, having hasted, and found both Mary, and Joseph, and the babe lying in the manger,
Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
17 and having seen, they made known abroad concerning the saying spoken to them concerning the child.
Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
18 And all who heard, did wonder concerning the things spoken by the shepherds unto them;
Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
19 and Mary was preserving all these things, pondering in her heart;
Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
20 and the shepherds turned back, glorifying and praising God, for all those things they heard and saw, as it was spoken unto them.
Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
21 And when eight days were fulfilled to circumcise the child, then was his name called Jesus, having been so called by the messenger before his being conceived in the womb.
Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
22 And when the days of their purification were fulfilled, according to the law of Moses, they brought him up to Jerusalem, to present to the Lord,
Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
23 as it hath been written in the Law of the Lord, — 'Every male opening a womb shall be called holy to the Lord,'
Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
24 and to give a sacrifice, according to that said in the Law of the Lord, 'A pair of turtle-doves, or two young pigeons.'
Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
25 And lo, there was a man in Jerusalem, whose name [is] Simeon, and this man is righteous and devout, looking for the comforting of Israel, and the Holy Spirit was upon him,
Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
26 and it hath been divinely told him by the Holy Spirit — not to see death before he may see the Christ of the Lord.
An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
27 And he came in the Spirit to the temple, and in the parents bringing in the child Jesus, for their doing according to the custom of the law regarding him,
Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
28 then he took him in his arms, and blessed God, and he said,
sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
29 'Now Thou dost send away Thy servant, Lord, according to Thy word, in peace,
“Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
30 because mine eyes did see Thy salvation,
Domin idanuna sun ga cetonka,
31 which Thou didst prepare before the face of all the peoples,
wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
32 a light to the uncovering of nations, and the glory of Thy people Israel.'
Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
33 And Joseph and his mother were wondering at the things spoken concerning him,
Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
34 and Simeon blessed them, and said unto Mary his mother, 'Lo, this [one] is set for the falling and rising again of many in Israel, and for a sign spoken against —
Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
35 (and also thine own soul shall a sword pass through) — that the reasonings of many hearts may be revealed.'
Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
36 And there was Anna, a prophetess, daughter of Phanuel, of the tribe of Asher, she was much advanced in days, having lived with an husband seven years from her virginity,
Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
37 and she [is] a widow of about eighty-four years, who did depart not from the temple, with fasts and supplications serving, night and day,
sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
38 and she, at that hour, having come in, was confessing, likewise, to the Lord, and was speaking concerning him, to all those looking for redemption in Jerusalem.
A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
39 And when they finished all things, according to the Law of the Lord, they turned back to Galilee, to their city Nazareth;
Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
40 and the child grew and was strengthened in spirit, being filled with wisdom, and the grace of God was upon him.
Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
41 And his parents were going yearly to Jerusalem, at the feast of the passover,
Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
42 and when he became twelve years old, they having gone up to Jerusalem, according to the custom of the feast,
Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
43 and having finished the days, in their returning the child Jesus remained behind in Jerusalem, and Joseph and his mother did not know,
Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
44 and, having supposed him to be in the company, they went a day's journey, and were seeking him among the kindred and among the acquaintances,
Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
45 and not having found him, they turned back to Jerusalem seeking him.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
46 And it came to pass, after three days, they found him in the temple, sitting in the midst of the teachers, both hearing them and questioning them,
Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
47 and all those hearing him were astonished at his understanding and answers.
Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
48 And, having seen him, they were amazed, and his mother said unto him, 'Child, why didst thou thus to us? lo, thy father and I, sorrowing, were seeking thee.'
Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
49 And he said unto them, 'Why [is it] that ye were seeking me? did ye not know that in the things of my Father it behoveth me to be?'
Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 and they did not understand the saying that he spake to them,
Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
51 and he went down with them, and came to Nazareth, and he was subject to them, and his mother was keeping all these sayings in her heart,
Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
52 and Jesus was advancing in wisdom, and in stature, and in favour with God and men.
Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.

< Luke 2 >