< Leviticus 18 >
1 And Jehovah speaketh unto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 'Speak unto the sons of Israel, and thou hast said unto them, I [am] Jehovah your God;
“Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
3 according to the work of the land of Egypt in which ye have dwelt ye do not, and according to the work of the land of Canaan whither I am bringing you in, ye do not, and in their statutes ye walk not.
Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
4 'My judgments ye do, and My statutes ye keep, to walk in them; I [am] Jehovah your God;
Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
5 and ye have kept My statutes and My judgments which man doth and liveth in them; I [am] Jehovah.
Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
6 'None of you unto any relation of his flesh doth draw near to uncover nakedness; I [am] Jehovah.
“‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
7 'The nakedness of thy father and the nakedness of thy mother thou dost not uncover, she [is] thy mother; thou dost not uncover her nakedness.
“‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
8 'The nakedness of the wife of thy father thou dost not uncover; it [is] the nakedness of thy father.
“‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
9 'The nakedness of thy sister, daughter of thy father, or daughter of thy mother, born at home or born without; thou dost not uncover their nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
10 'The nakedness of thy son's daughter, or of thy daughter's daughter: thou dost not uncover their nakedness; for theirs [is] thy nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
11 'The nakedness of a daughter of thy father's wife, begotten of thy father, she [is] thy sister; thou dost not uncover her nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
12 'The nakedness of a sister of thy father thou dost not uncover; she [is] a relation of thy father.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
13 'The nakedness of thy mother's sister thou dost not uncover; for she [is] thy mother's relation.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
14 'The nakedness of thy father's brother thou dost not uncover; unto his wife thou dost not draw near; she [is] thine aunt.
“‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
15 'The nakedness of thy daughter-in-law thou dost not uncover; she [is] thy son's wife; thou dost not uncover her nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
16 'The nakedness of thy brother's wife thou dost not uncover; it [is] thy brother's nakedness.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
17 'The nakedness of a woman and her daughter thou dost not uncover; her son's daughter, and her daughter's daughter thou dost not take to uncover her nakedness; they [are] her relations; it [is] wickedness.
“‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
18 'And a woman unto another thou dost not take, to be an adversary, to uncover her nakedness beside her, in her life.
“‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
19 'And unto a woman in the separation of her uncleanness thou dost not draw near to uncover her nakedness.
“‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
20 'And unto the wife of thy fellow thou dost not give thy seed of copulation, for uncleanness with her.
“‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
21 'And of thy seed thou dost not give to pass over to the Molech; nor dost thou pollute the name of thy God; I [am] Jehovah.
“‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
22 'And with a male thou dost not lie as one lieth with a woman; abomination it [is].
“‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
23 'And with any beast thou dost not give thy copulation, for uncleanness with it; and a woman doth not stand before a beast to lie down with it; confusion it [is].
“‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
24 'Ye are not defiled with all these, for with all these have the nations been defiled which I am sending away from before you;
“‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
25 and the land is defiled, and I charge its iniquity upon it, and the land vomiteth out its inhabitants:
Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
26 and ye — ye have kept My statutes and My judgments, and do not [any] of all these abominations, the native and the sojourner who is sojourning in your midst,
Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
27 (for all these abominations have the men of the land done who [are] before you, and the land is defiled),
gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
28 and the land doth not vomit you out in your defiling it, as it hath vomited out the nation which [is] before you;
Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
29 for any one who doth [any] of all these abominations — even the persons who are doing [so], have been cut off from the midst of their people;
“‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
30 and ye have kept My charge, so as not to do [any] of the abominable statutes which have been done before you, and ye do not defile yourselves with them; I [am] Jehovah your God.'
Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”