< Leviticus 14 >
1 And Jehovah speaketh unto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 'This is a law of the leper, in the day of his cleansing, that he hath been brought in unto the priest,
“Waɗannan su ne ƙa’idodi domin mutumin da yake da cuta a lokacin tsabtaccewarsa, sa’ad da aka kawo shi ga firist.
3 and the priest hath gone out unto the outside of the camp, and the priest hath seen, and lo, the plague of leprosy hath ceased from the leper,
Firist zai fita waje da sansani ya bincike shi. In mutumin ya warke daga cutar fatar jiki mai yaɗuwa,
4 and the priest hath commanded, and he hath taken for him who is to be cleansed, two clean living birds, and cedar wood, and scarlet, and hyssop.
firist zai umarta a kawo tsuntsaye biyu masu rai, masu tsabta da itacen al’ul, jan ƙyalle da kuma hizzob saboda mutumin da za a tsabtacce.
5 'And the priest hath commanded, and he hath slaughtered the one bird upon an earthen vessel, over running water;
Sa’an nan firist zai umarta a kashe ɗaya daga cikin tsuntsayen a bisa ruwa mai kyau a tukunyar laka.
6 [as to] the living bird, he taketh it, and the cedar wood, and the scarlet, and the hyssop, and hath dipped them and the living bird in the blood of the slaughtered bird, over the running water,
Zai ɗauki tsuntsu mai rai ya tsoma shi tare da itacen al’ul, jan ƙyalle da kuma hizzob cikin jinin tsuntsun da aka yanka a bisa ruwa mai kyau.
7 and he hath sprinkled on him who is to be cleansed from the leprosy seven times, and hath pronounced him clean, and hath sent out the living bird on the face of the field.
Sau bakwai zai yayyafa wa mutumin da za a tsabtacce daga cutar mai yaɗuwa ya kuma furta shi tsarkakakke. Sa’an nan ya saki tsuntsu mai rai ɗin ya tafi.
8 'And he who is to be cleansed hath washed his garments, and hath shaved all his hair, and hath bathed with water, and hath been clean, and afterwards he doth come in unto the camp, and hath dwelt at the outside of his tent seven days.
“Dole mutumin da aka tsabtaccen ya wanke rigunansa, ya aske dukan gashinsa ya kuma yi wanka; sa’an nan zai tsabtacce. Bayan wannan zai iya zo cikin sansani, amma dole yă tsaya waje da tentinsa kwana bakwai.
9 'And it hath been, on the seventh day — he shaveth all his hair, his head, and his beard, and his eyebrows, even all his hair he doth shave, and he hath washed his garments, and hath bathed his flesh with water, and hath been clean.
A rana ta bakwai ɗin dole yă aske dukan gashinsa; dole yă aske kansa, gemunsa, gashin girarsa da sauran gashinsa. Dole yă wanke rigunansa ya kuma yi wanka, zai kuwa tsabtacce.
10 'And on the eighth day he taketh two lambs, perfect ones, and one ewe-lamb, daughter of a year, a perfect one, and three tenth deals of flour [for] a present, mixed with oil, and one log of oil.
“A rana ta takwas dole yă kawo ɗan rago da’yar tunkiya bana ɗaya, kowane marar lahani, tare da rabin garwan gari mai laushi haɗe da mai domin hadaya ta gari, da kuma moɗa ɗaya na mai.
11 'And the priest who is cleansing hath caused the man who is to be cleansed to stand with them before Jehovah, at the opening of the tent of meeting,
Firist da ya furta shi tsarkakakke zai miƙa da wanda za a tsabtaccen da kuma hadayunsa a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
12 and the priest hath taken the one he-lamb, and hath brought it near for a guilt-offering, also the log of oil, and hath waved them — a wave offering before Jehovah.
“Sa’ad da firist zai ɗauki ɗaya daga cikin ragunan ya kuma miƙa shi kamar hadaya don laifi, tare da moɗan mai; zai kaɗa su a gaban Ubangiji kamar hadaya kaɗawa.
13 'And he hath slaughtered the lamb in the place where he slaughtereth the sin-offering and the burnt-offering, in the holy place; for like the sin-offering the guilt-offering is to the priest; it [is] most holy.
Zai yanka ɗan ragon a tsattsarkan wuri inda ake yanka hadaya don zunubi da hadaya ta ƙonawa. Gama yadda hadaya ta zunubi ta firist ne, haka hadaya domin laifi ma, hadaya ce mafi tsarki.
14 'And the priest hath taken of the blood of the guilt-offering, and the priest hath put on the tip of the right ear of him who is to be cleansed, and on the thumb of his right hand, and on the great toe of his right foot;
Firist ɗin zai ɗiba jinin hadaya don laifin ya zuba a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsabtacce, a babbar yatsar hannunsa na dama a kuma a babbar yatsar ƙafa damansa.
15 and the priest hath taken of the log of oil, and hath poured on the left palm of the priest,
Firist ɗin zai ɗiba daga moɗan mai ɗin ya zuba a tafin hannunsa na hagu,
16 and the priest hath dipped his right finger in the oil which [is] on his left palm, and hath sprinkled of the oil with his finger seven times before Jehovah.
ya tsoma yatsarsa ta dama cikin man da yake a tafin hannunsa, kuma da yatsar zai yayyafa man a gaban Ubangiji sau bakwai.
17 'And of the residue of the oil which [is] on his palm, the priest putteth on the tip of the right ear of him who is to be cleansed, and on the thumb of his right hand, and on the great toe of his right foot, on the blood of the guilt-offering;
Firist zai sa sauran mai da yake cikin tafinsa a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsabtacce, a babbar yatsarsa na dama da kuma a babbar yatsar ƙafarsa ta dama, a bisa jinin hadaya don laifin.
18 and the remnant of the oil which [is] on the palm of the priest, he putteth on the head of him who is to be cleansed, and the priest hath made atonement for him before Jehovah.
Sauran man a tafin hannunsa firist zai sa a kan wanda za a tsabtaccen ya kuma yi kafara dominsa a gaban Ubangiji.
19 'And the priest hath made the sin-offering, and hath made atonement for him who is to be cleansed from his uncleanness, and afterwards he doth slaughter the burnt-offering;
“Sa’an nan firist ɗin zai miƙa hadaya don zunubi ya kuma yi kafara saboda wannan da za a tsabtacce daga rashin tsarkinsa. Bayan haka, firist zai yanka hadaya ta ƙonawa
20 and the priest hath caused the burnt-offering to ascend, also the present, on the altar, and the priest hath made atonement for him, and he hath been clean.
ya miƙa ta a bagade, tare da hadaya ta gari, ya kuma yi kafara dominsa, zai kuwa tsabtacce.
21 'And if he [is] poor, and his hand is not reaching [these things], then he hath taken one lamb — a guilt-offering, for a wave-offering, to make atonement for him, and one-tenth deal of flour mixed with oil for a present, and a log of oil,
“In kuwa mutumin matalauci ne ba zai iya samu waɗannan ba, to, dole yă ɗauki ɗan rago guda kamar hadaya don laifi a kaɗa don a yi kafara dominsa, tare da humushin garwa gari mai laushi haɗe da mai don hadaya ta gari, da moɗa na mai,
22 and two turtle-doves, or two young pigeons, which his hand reacheth to, and one hath been a sin-offering, and the one a burnt-offering;
da kurciyoyi biyu ko tattabarai biyu, wanda zai iya samu, ɗaya domin hadaya don zunubi ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa.
23 and he hath brought them in on the eighth day for his cleansing unto the priest, unto the opening of the tent of meeting, before Jehovah.
“A rana ta takwas dole yă kawo su domin tsabtaccewarsa ga firist a ƙofar Tentin Sujada, a gaban Ubangiji.
24 'And the priest hath taken the lamb of the guilt-offering, and the log of oil, and the priest hath waved them — a wave-offering before Jehovah;
Firist zai ɗauki ɗan rago na hadaya don laifi tare da moɗa na mai, ya kaɗa su a gaban Ubangiji kamar hadaya ta kaɗawa.
25 and he hath slaughtered the lamb of the guilt-offering, and the priest hath taken of the blood of the guilt-offering, and hath put on the tip of the right ear of him who is to be cleansed, and on the thumb of his right hand, and on the great toe of his right foot;
Zai yanka ɗan rago domin hadaya don laifi ya kuma ɗibi jinin ya sa a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsabtaccen, a babban yatsar hannun damansa da kuma a babban yatsar ƙafarsa na dama.
26 and the priest doth pour of the oil on the left palm of the priest;
Firist zai zuba man a tafin hannunsa na hagu,
27 and the priest hath sprinkled with his right finger of the oil which [is] on his left palm, seven times before Jehovah.
da yatsarsa na dama zai yayyafa man daga tafinsa sau bakwai a gaban Ubangiji.
28 'And the priest hath put of the oil which [is] on his palm, on the tip of the right ear of him who is to be cleansed, and on the thumb of his right hand, and on the great toe of his right foot, on the place of the blood of the guilt-offering;
Daga cikin man da yake a tafinsa zai zuba a wuri da ya zuba jinin hadaya don laifi, a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsabtaccen, a babban yatsar hannun damansa da kuma a babban yatsar ƙafa damansa.
29 and the remnant of the oil which [is] on the palm of the priest he doth put on the head of him who is to be cleansed, to make atonement for him, before Jehovah.
Sauran man da yake cikin tafinsa firist ɗin zai zuba a kan wannan da za a tsabtaccen don a yi kafara dominsa a gaban Ubangiji.
30 'And he hath made the one of the turtle-doves, or of the young pigeons (from that which his hand reacheth to,
Sa’an nan zai miƙa kurciyoyi ko tattabarai, waɗanda mutumin zai iya,
31 [even] that which his hand reacheth to), the one a sin-offering, and the one a burnt offering, besides the present, and the priest hath made atonement for him who is to be cleansed before Jehovah.
ɗaya kamar hadaya don zunubi ɗayan kuma kamar hadaya ta ƙonawa, tare da hadaya ta gari. Ta haka firist zai yi kafara a gaban Ubangiji a madadin wanda za a tsabtacce.”
32 This [is] a law of him in whom [is] a plague of leprosy, whose hand reacheth not to his cleansing.'
Waɗannan su ne ƙa’idodi domin mutumin da yake da cutar fatar jiki wanda kuma ba zai iya samun abubuwan hadaya ta kullum domin tsabtaccewarsa ba.
33 And Jehovah speaketh unto Moses, and unto Aaron, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
34 'When ye come in unto the land of Canaan, which I am giving to you for a possession, and I have put a plague of leprosy in a house [in] the land of your possession;
“Sa’ad da kuka shiga ƙasar Kan’ana, wadda nake ba ku kamar gādonku, na kuma sa yaɗuwa cutar fatar jiki a riga a cikin gida a wannan ƙasa,
35 then hath he whose the house [is] come in and declared to the priest, saying, As a plague hath appeared to me in the house;
dole maigidan ya tafi ya faɗa wa firist ya ce, ‘Na ga wani abu da ya yi kamar cutar fatar jikin da take a riga a cikin gidana.’
36 and the priest hath commanded, and they have prepared the house before the priest cometh in to see the plague (that all which [is] in the house be not unclean), and afterwards doth the priest come in to see the house;
Firist zai umarci a fitar da kome a gidan kafin ya shiga ya bincike cutar fatar jiki da take a rigar, saboda babu abin da yake gidan da za a furta marar tsarki ne. Bayan haka firist zai shiga ya dudduba gidan.
37 and he hath seen the plague, and lo, the plague [is] in the walls of the house, hollow strakes, very green or very red, and their appearance [is] lower than the wall,
Zai bincike cutar fatar jiki da take a riga a bangaye, in kuma yana da tabon kore-kore ko ja-ja da suka bayyana da suka yi zurfi fiye da saman bangon,
38 and the priest hath gone out of the house unto the opening of the house, and hath shut up the house seven days.
firist ɗin zai fita a bakin ƙofar gidan ya rufe ta na kwana bakwai.
39 'And the priest hath turned back on the seventh day, and hath seen, and lo, the plague hath spread in the walls of the house,
A rana ta bakwai ɗin firist zai dawo don yă dudduba gidan. In cutar fatar jiki da take a riga ta yaɗu a bangayen,
40 and the priest hath commanded, and they have drawn out the stones in which the plague [is], and have cast them unto the outside of the city, unto an unclean place;
zai umarta a ciccire duwatsun da suke da cutar a zubar a wuri marar tsarki waje da birnin.
41 and the house he doth cause to be scraped within round about, and they have poured out the clay which they have scraped off, at the outside of the city, at an unclean place;
Dole yă sa a kankare duka shafen bangon cikin gidan a kuma zuba kayan da aka kankare a wurin marar tsarki waje da birnin.
42 and they have taken other stones, and brought [them] in unto the place of the stones, and other clay he taketh and hath daubed the house.
Sai su ɗebi waɗansu duwatsu su sa a wuraren da suka ciccire waɗancan, su kuma ɗiba sabon laka su yi shafen gidan.
43 'And if the plague return, and hath broken out in the house, after he hath drawn out the stones, and after the scraping of the house, and after the daubing;
“In cutar fatar jiki da take ta rigar ta sāke bayyana a gidan bayan an ciccire duwatsu aka kankare gidan aka kuma yi shafe,
44 then hath the priest come in and seen, and lo, the plague hath spread in the house; it [is] a fretting leprosy in the house; it [is] unclean.
firist zai je ya bincika shi, in kuwa cutar ta bazu a gidan, to, muguwar cuta ce; gidan marar tsarki ne.
45 'And he hath broken down the house, its stones, and its wood, and all the clay of the house, and he hath brought [them] forth unto the outside of the city, unto an unclean place.
Dole a rushe gidan, a fid da duwatsun, katakai da kuma dukan shafen daga birnin zuwa wuri marar tsarki.
46 'And he who is going in unto the house all the days he hath shut it up, is unclean till the evening;
“Duk wanda ya shiga gidan yayinda aka rufe shi zai ƙazantu har yamma.
47 and he who is lying in the house doth wash his garments; and he who is eating in the house doth wash his garments.
Duk wanda ya kwana ko ya ci abinci a gidan dole yă wanke rigunansa.
48 'And if the priest certainly come in, and hath seen, and lo, the plague hath not spread in the house after the daubing of the house, then hath the priest pronounced the house clean, for the plague hath been healed.
“Amma in firist ya zo ya bincika gidan kuma cutar fatar jiki da take ta rigar ba tă bazu ba bayan an yi wa gidan shafe, zai furta gidan tsarkakakke, domin cutar ta tafi.
49 'And he hath taken for the cleansing of the house two birds, and cedar wood, and scarlet, and hyssop;
Don a tsabtacce gidan, zai ɗauki tsuntsaye biyu da itacen al’ul, jan ƙyalle da hizzob.
50 and he hath slaughtered the one bird upon an earthen vessel, over running water;
Zai yanka ɗaya daga cikin tsuntsayen a bisa ruwa mai kyau a cikin tukunyar laka.
51 and he hath taken the cedar wood, and the hyssop, and the scarlet, and the living bird, and hath dipped them in the blood of the slaughtered bird, and in the running water, and hath sprinkled upon the house seven times.
Sa’an nan zai ɗauki itacen al’ul, hizzob, jan ƙyalle da kuma tsuntsu mai ran ya tsoma su cikin jinin tsuntsun da aka yanka da kuma cikin ruwa mai kyau, ya yayyafa wa gida sau bakwai.
52 'And he hath cleansed the house with the blood of the bird, and with the running water, and with the living bird, and with the cedar wood, and with the hyssop, and with the scarlet;
Zai tsabtacce gidan da jinin tsuntsun, ruwa mai kyau, tsuntsu mai ran, itacen al’ul, hizzob da kuma jan ƙyalle.
53 and he hath sent away the living bird unto the outside of the city unto the face of the field, and hath made atonement for the house, and it hath been clean.
Sa’an nan zai saki tsuntsu mai rai ɗin a fili waje da birnin ya tafi. Ta haka zai yi kafara saboda gidan, gidan kuwa zai zama tsarkakakke.”
54 'This [is] the law for every plague of the leprosy and for scall,
Waɗannan su ne ƙa’idodi saboda duk wani cuta mai yaɗuwa, don ƙaiƙayi,
55 and for leprosy of a garment, and of a house,
don cutar fatar jiki da take a riga ko a cikin gida,
56 and for a rising, and for a scab, and for a bright spot, —
da kuma don kumburi, ɓamɓaroki ko tabo,
57 to direct in the day of being unclean, and in the day of being clean; this [is] the law of the leprosy.'
don a tabbatar sa’ad da wani abu mai tsarki da marar tsarki. Waɗannan su ne ƙa’idodi domin cutar fatar jiki mai yaɗuwa da cutar fatar jikin da take a riga.