< John 2 >
1 And the third day a marriage happened in Cana of Galilee, and the mother of Jesus was there,
Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin.
2 and also Jesus was called, and his disciples, to the marriage;
An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
3 and wine having failed, the mother of Jesus saith unto him, 'Wine they have not;'
Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
4 Jesus saith to her, 'What — to me and to thee, woman? not yet is mine hour come.'
Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
5 His mother saith to the ministrants, 'Whatever he may say to you — do.'
Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
6 And there were there six water-jugs of stone, placed according to the purifying of the Jews, holding each two or three measures.
To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
7 Jesus saith to them, 'Fill the water-jugs with water;' and they filled them — unto the brim;
Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.
8 and he saith to them, 'Draw out, now, and bear to the director of the apartment;' and they bare.
Sai yace wa ma'aikatan, “Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki.” Sai suka yi hakannan.
9 And as the director of the apartment tasted the water become wine, and knew not whence it is, (but the ministrants knew, who have drawn the water, ) the director of the feast doth call the bridegroom,
Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango
10 and saith to him, 'Every man, at first, the good wine doth set forth; and when they may have drunk freely, then the inferior; thou didst keep the good wine till now.'
yace masa, “Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu.”
11 This beginning of the signs did Jesus in Cana of Galilee, and manifested his glory, and his disciples believed in him;
Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
12 after this he went down to Capernaum, he, and his mother, and his brethren, and his disciples; and there they remained not many days.
Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13 And the passover of the Jews was nigh, and Jesus went up to Jerusalem,
To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
14 and he found in the temple those selling oxen, and sheep, and doves, and the money-changers sitting,
Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15 and having made a whip of small cords, he put all forth out of the temple, also the sheep, and the oxen; and of the money-changers he poured out the coins, and the tables he overthrew,
Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
16 and to those selling the doves he said, 'Take these things hence; make not the house of my Father a house of merchandise.'
Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
17 And his disciples remembered that it is written, 'The zeal of Thy house did eat me up;'
Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”
18 the Jews then answered and said to him, 'What sign dost thou shew to us — that thou dost these things?'
Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?”
19 Jesus answered and said to them, 'Destroy this sanctuary, and in three days I will raise it up.'
Yesu ya amsa, “Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi.”
20 The Jews, therefore, said, 'Forty and six years was this sanctuary building, and wilt thou in three days raise it up?'
Sai shugabanin Yahudawa suka ce, “An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?”
21 but he spake concerning the sanctuary of his body;
Amma yana nufin haikali na jikinsa ne.
22 when, then, he was raised out of the dead, his disciples remembered that he said this to them, and they believed the Writing, and the word that Jesus said.
Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
23 And as he was in Jerusalem, in the passover, in the feast, many believed in his name, beholding his signs that he was doing;
Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi.
24 and Jesus himself was not trusting himself to them, because of his knowing all [men],
Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka,
25 and because he had no need that any should testify concerning man, for he himself was knowing what was in man.
saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.