< Job 36 >
1 And Elihu addeth and saith: —
Elihu ya ci gaba,
2 Honour me a little, and I shew thee, That yet for God [are] words.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 I lift up my knowledge from afar, And to my Maker I ascribe righteousness.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 For, truly, my words [are] not false, The perfect in knowledge [is] with thee.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Lo, God [is] mighty, and despiseth not, Mighty [in] power [and] heart.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 He reviveth not the wicked, And the judgment of the poor appointeth;
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 He withdraweth not from the righteous His eyes, And [from] kings on the throne, And causeth them to sit for ever, and they are high,
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 And if prisoners in fetters They are captured with cords of affliction,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 Then He declareth to them their work, And their transgressions, Because they have become mighty,
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 And He uncovereth their ear for instruction, And saith that they turn back from iniquity.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 If they do hear and serve, They complete their days in good, And their years in pleasantness.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 And if they do not hearken, By the dart they pass away, And expire without knowledge.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 And the profane in heart set the face, They cry not when He hath bound them.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Their soul dieth in youth, And their life among the defiled.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 He draweth out the afflicted in his affliction, And uncovereth in oppression their ear.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 And also He moved thee from a strait place, [To] a broad place — no straitness under it, And the sitting beyond of thy table Hath been full of fatness.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 And the judgment of the wicked thou hast fulfilled, Judgment and justice are upheld — because of fury,
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Lest He move thee with a stroke, And the abundance of an atonement turn thee not aside.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Doth He value thy riches? He hath gold, and all the forces of power.
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Desire not the night, For the going up of peoples in their stead.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Take heed — do not turn unto iniquity, For on this thou hast fixed Rather than [on] affliction.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Lo, God doth sit on high by His power, Who [is] like Him — a teacher?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Who hath appointed unto Him his way? And who said, 'Thou hast done iniquity?'
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Remember that thou magnify His work That men have beheld.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 All men have looked on it, Man looketh attentively from afar.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Lo, God [is] high, And we know not the number of His years, Yea, there [is] no searching.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 When He doth diminish droppings of the waters, They refine rain according to its vapour,
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Which clouds do drop, They distil on man abundantly.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Yea, doth [any] understand The spreadings out of a cloud? The noises of His tabernacle?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Lo, He hath spread over it His light, And the roots of the sea He hath covered,
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 For by them He doth judge peoples, He giveth food in abundance.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 By two palms He hath covered the light, And layeth a charge over it in meeting,
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 He sheweth by it [to] his friend substance, Anger against perversity.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.