< Job 32 >
1 And these three men cease from answering Job, for he [is] righteous in his own eyes,
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 and burn doth the anger of Elihu son of Barachel the Buzite, of the family of Ram; against Job hath his anger burned, because of his justifying himself more than God;
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 and against his three friends hath his anger burned, because that they have not found an answer, and condemn Job.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 And Elihu hath waited earnestly beside Job with words, for they are older than he in days.
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 And Elihu seeth that there is no answer in the mouth of the three men, and his anger burneth.
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 And Elihu son of Barachel the Buzite answereth and saith: — Young I [am] in days, and ye [are] age Therefore I have feared, And am afraid of shewing you my opinion.
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 I said: Days do speak, And multitude of years teach wisdom.
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 Surely a spirit is in man, And the breath of the Mighty One Doth cause them to understand.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 The multitude are not wise, Nor do the aged understand judgment.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 Therefore I have said: Hearken to me, I do shew my opinion — even I.
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 Lo, I have waited for your words, I give ear unto your reasons, Till ye search out sayings.
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 And unto you I attend, And lo, there is no reasoner for Job, [Or] answerer of his sayings among you.
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 Lest ye say, We have found wisdom, God doth thrust him away, not man.
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 And he hath not set in array words for me, And with your sayings I do not answer him.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 (They have broken down, They have not answered again, They removed from themselves words.
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 And I have waited, but they do not speak, For they have stood still, They have not answered any more.)
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 I answer, even I — my share, I shew my opinion — even I.
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 For I have been full of words, Distressed me hath the spirit of my breast,
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 Lo, my breast [is] as wine not opened, Like new bottles it is broken up.
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 I speak, and there is refreshment to me, I open my lips and answer.
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 Let me not, I pray you, accept the face of any, Nor unto man give flattering titles,
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 For I have not known to give flattering titles, In a little doth my Maker take me away.
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.