< Job 23 >

1 And Job answereth and saith: —
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Also — to-day [is] my complaint bitter, My hand hath been heavy because of my sighing.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3 O that I had known — and I find Him, I come in unto His seat,
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4 I arrange before Him the cause, And my mouth fill [with] arguments.
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5 I know the words He doth answer me, And understand what He saith to me.
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6 In the abundance of power doth He strive with me? No! surely He putteth [it] in me.
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7 There the upright doth reason with Him, And I escape for ever from my judge.
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
8 Lo, forward I go — and He is not, And backward — and I perceive him not.
“Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
9 [To] the left in His working — and I see not, He is covered [on] the right, and I behold not.
Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
10 For He hath known the way with me, He hath tried me — as gold I go forth.
Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
11 On His step hath my foot laid hold, His way I have kept, and turn not aside,
Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
12 The command of His lips, and I depart not. Above my allotted portion I have laid up The sayings of His mouth.
Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
13 And He [is] in one [mind], And who doth turn Him back? And His soul hath desired — and He doth [it].
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14 For He doth complete my portion, And many such things [are] with Him.
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15 Therefore, from His presence I am troubled, I consider, and am afraid of Him.
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16 And God hath made my heart soft, And the Mighty hath troubled me.
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17 For I have not been cut off before darkness, And before me He covered thick darkness.
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.

< Job 23 >