< Job 21 >

1 And Job answereth and saith: —
Sai Ayuba ya amsa,
2 Hear ye diligently my word, And this is your consolation.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Bear with me, and I speak, And after my speaking — ye may deride.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 I — to man [is] my complaint? and if [so], wherefore May not my temper become short?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Turn unto me, and be astonished, And put hand to mouth.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Yea, if I have remembered, then I have been troubled. And my flesh hath taken fright.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Wherefore do the wicked live? They have become old, Yea, they have been mighty in wealth.
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Their seed is established, Before their face with them, And their offspring before their eyes.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Their houses [are] peace without fear, Nor [is] a rod of God upon them.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 His bullock hath eaten corn, and doth not loath. His cow bringeth forth safely, And doth not miscarry.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 They send forth as a flock their sucklings, And their children skip,
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 They lift [themselves] up at timbrel and harp, And rejoice at the sound of an organ.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 They wear out in good their days, And in a moment [to] Sheol go down. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 And they say to God, 'Turn aside from us, And the knowledge of Thy ways We have not desired.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 What [is] the Mighty One that we serve Him? And what do we profit when we meet with Him?'
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Lo, not in their hand [is] their good, (The counsel of the wicked Hath been far from me.)
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 How oft is the lamp of the wicked extinguished, And come on them doth their calamity? Pangs He apportioneth in His anger.
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 They are as straw before wind, And as chaff a hurricane hath stolen away,
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 God layeth up for his sons his sorrow, He giveth recompense unto him — and he knoweth.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 His own eyes see his destruction, And of the wrath of the Mighty he drinketh.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 For what [is] his delight in his house after him, And the number of his months cut off?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 To God doth [one] teach knowledge, And He the high doth judge?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 This [one] dieth in his perfect strength, Wholly at ease and quiet.
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 His breasts have been full of milk, And marrow his bones doth moisten.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 And this [one] dieth with a bitter soul, And have not eaten with gladness.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Together — on the dust they lie down, And the worm doth cover them over.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Lo, I have known your thoughts, And the devices against me ye do wrongfully.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 For ye say, 'Where [is] the house of the noble? And where the tent — The tabernacles of the wicked?'
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Have ye not asked those passing by the way? And their signs do ye not know?
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 That to a day of calamity is the wicked spared. To a day of wrath they are brought.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Who doth declare to his face his way? And [for] that which he hath done, Who doth give recompence to him?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 And he — to the graves he is brought. And over the heap a watch is kept.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 Sweet to him have been the clods of the valley, And after him every man he draweth, And before him there is no numbering.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 And how do ye comfort me [with] vanity, And in your answers hath been left trespass?
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >