< Job 13 >
1 Lo, all — hath mine eye seen, Heard hath mine ear, and it attendeth to it.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 According to your knowledge I have known — also I. I am not fallen more than you.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Yet I for the Mighty One do speak, And to argue for God I delight.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 And yet, ye [are] forgers of falsehood, Physicians of nought — all of you,
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 O that ye would keep perfectly silent, And it would be to you for wisdom.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Hear, I pray you, my argument, And to the pleadings of my lips attend,
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 For God do ye speak perverseness? And for Him do ye speak deceit?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 His face do ye accept, if for God ye strive?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Is [it] good that He doth search you, If, as one mocketh at a man, ye mock at Him?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 He doth surely reprove you, if in secret ye accept faces.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Doth not His excellency terrify you? And His dread fall upon you?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Your remembrances [are] similes of ashes, For high places of clay your heights.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Keep silent from me, and I speak, And pass over me doth what?
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Wherefore do I take my flesh in my teeth? And my soul put in my hand?
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Lo, He doth slay me — I wait not! Only, my ways unto His face I argue.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Also — He [is] to me for salvation, For the profane cometh not before Him.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Hear ye diligently my word, And my declaration with your ears.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Lo, I pray you, I have set in order the cause, I have known that I am righteous.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Who [is] he that doth strive with me? For now I keep silent and gasp.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Only two things, O God, do with me: Then from Thy face I am not hidden.
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Thy hand put far off from me, And Thy terror let not terrify me.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 And call Thou, and I — I answer, Or — I speak, and answer Thou me.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 How many iniquities and sins have I? My transgression and my sin let me know.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Why dost Thou hide Thy face? And reckonest me for an enemy to Thee?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 A leaf driven away dost Thou terrify? And the dry stubble dost Thou pursue?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 For Thou writest against me bitter things, And causest me to possess iniquities of my youth:
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 And puttest in the stocks my feet, And observest all my paths, On the roots of my feet Thou settest a print,
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 And he, as a rotten thing, weareth away, As a garment hath a moth consumed him.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.