< Jeremiah 25 >

1 The word that hath been unto Jeremiah concerning all the people of Judah, in the fourth year of Jehoiakim son of Josiah king of Judah, — it [is] the first year of Nebuchadrezzar king of Babylon, —
Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
2 Which Jeremiah the prophet hath spoken concerning all the people of Judah, even unto all the inhabitants of Jerusalem, saying:
Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
3 'From the thirteenth year of Josiah son of Amon king of Judah, and unto this day — this three and twentieth year — hath the word of Jehovah been unto me, and I speak unto you, rising early and speaking, and ye have not hearkened;
Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
4 And Jehovah hath sent unto you all His servants, the prophets, rising early and sending, and ye have not hearkened, nor inclined your ear to hear, saying:
Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
5 'Turn back, I pray you, each from his evil way, and from the evil of your doings, and dwell on the ground that Jehovah hath given to you and to your fathers from age unto age,
Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
6 And ye do not go after other gods to serve them, and to bow yourselves to them, nor do ye provoke Me to anger with the work of your hands, and I do no evil to you;
Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
7 And ye have not hearkened unto Me — an affirmation of Jehovah — so as to provoke Me to anger with the work of your hands for evil to you.
“Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
8 'Therefore thus said Jehovah of Hosts, Because that ye have not obeyed My words,
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
9 Lo, I am sending, and have taken all the families of the north — an affirmation of Jehovah — even unto Nebuchadrezzar king of Babylon, My servant, and have brought them in against this land, and against its inhabitants, and against all these nations round about, and have devoted them, and appointed them for an astonishment, and for a hissing, and for wastes age-during.
zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
10 And I have destroyed from them the voice of rejoicing, and the voice of joy, voice of bridegroom and voice of bride, noise of millstones, and the light of lamps.
Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
11 And all this land hath been for a waste, for an astonishment, and these nations have served the king of Babylon seventy years.
Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
12 'And it hath come to pass, at the fulness of seventy years, I charge against the king of Babylon, and against that nation — an affirmation of Jehovah — their iniquity, and against the land of the Chaldeans, and have appointed it for desolations age-during.
“Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
13 And I have brought in on that land all My words that I have spoken against it, all that is written in this book, that Jeremiah hath prophesied concerning all the nations.
Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
14 For laid service on them — also them — have many nations and great kings, and I have given recompence to them according to their doing, and according to the work of their hands.
Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
15 'For thus said Jehovah God of Israel unto me, Take the wine cup of this fury out of My hand, and thou hast caused all the nations to drink it unto whom I am sending thee;
Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
16 And they have drunk, and shaken themselves and shewn themselves foolish, because of the sword that I am sending among them.
Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
17 'And I take the cup out of the hand of Jehovah, and cause all the nations to drink unto whom Jehovah sent me:
Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
18 Jerusalem, and the cities of Judah, And its kings, its heads, To give them to waste, to astonishment, To hissing, and to reviling, as [at] this day.
Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
19 Pharaoh king of Egypt, and his servants, And his heads, and all his people,
Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
20 And all the mixed people, And all the kings of the land of Uz, And all the kings of the land of the Philistines, And Ashkelon, and Gazzah, and Ekron, And the remnant of Ashdod,
da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
21 Edom, and Moab, and the sons of Ammon,
Edom, Mowab da Ammon;
22 And all the kings of Tyre, And all the kings of Zidon, And the kings of the isle that [is] beyond the sea,
dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
23 Dedan, and Tema, and Buz, And all cutting the corners [of the beard],
Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
24 And all the kings of Arabia, And all the kings of the mixed people, Who are dwelling in the wilderness,
dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
25 And all the kings of Zimri, And all the kings of Elam, And all the kings of Media,
dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
26 And all the kings of the north, The near and the far off, one unto another, And all the kingdoms of the earth, That [are] on the face of the ground, And king Sheshach drinketh after them.
da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
27 And thou hast said unto them: Thus said Jehovah of Hosts God of Israel, Drink ye, yea drink abundantly, And vomit, and fall, and rise not, Because of the sword that I am sending among you.
“Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
28 And it hath come to pass, When they refuse to receive the cup out of thy hand to drink, That thou hast said unto them: Thus said Jehovah of Hosts, Ye do certainly drink.
Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
29 For lo, in the city over which My name is called, I am beginning to do evil, And ye — ye are entirely acquitted! Ye are not acquitted, for a sword I am proclaiming, For all inhabitants of the land, An affirmation of Jehovah of Hosts.
Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
30 And thou, thou dost prophesy unto them all these words, and hast said unto them: Jehovah from the high place doth roar, And from His holy habitation giveth forth His voice, He surely roareth for His habitation, A shout as of treaders down, God answereth all the inhabitants of the land,
“Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
31 Wasting hath come unto the end of the earth, For a controversy hath Jehovah with nations, He hath executed judgment for all flesh, The wicked! He hath given them to the sword, An affirmation of Jehovah.
Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
32 Thus said Jehovah of Hosts: Lo, evil is going out from nation to nation, And a great whirlwind is stirred up from the sides of the earth.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
33 And the pierced of Jehovah have been in that day, From the end of the earth even unto the end of the earth, They are not lamented, nor gathered, nor buried, For dung on the face of the ground they are.
A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
34 Howl, ye shepherds, and cry, And roll yourselves, ye honourable of the flock, For full have been your days, For slaughtering, and [for] your scatterings, And ye have fallen as a desirable vessel.
Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
35 And perished hath refuge from the shepherds, And escape from the honourable of the flock.
Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
36 A voice [is] of the cry of the shepherds, And a howling of the honourable of the flock, For Jehovah is spoiling their pasture.
Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
37 And the peaceable habitations have been cut down, Because of the fierceness of the anger of Jehovah.
Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
38 He hath forsaken, as a young lion, His covert, Surely their land hath become a desolation, Because of the oppressing fierceness, And because of the fierceness of His anger!
Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.

< Jeremiah 25 >