< James 2 >
1 My brethren, hold not, in respect of persons, the faith of the glory of our Lord Jesus Christ,
Ya ku 'yan'uwana, muddin kuna rike da bangaskiyar ku ga Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangijin daukaka, kada ku nuna bambanci ga wadansu mutane.
2 for if there may come into your synagogue a man with gold ring, in gay raiment, and there may come in also a poor man in vile raiment,
Idan wani mutum ya halarci taron ku da zobban zinariya da tufafi masu kyau, wani matalauci kuma ya shigo da tufafi marasa tsabta.
3 and ye may look upon him bearing the gay raiment, and may say to him, 'Thou — sit thou here well,' and to the poor man may say, 'Thou — stand thou there, or, Sit thou here under my footstool,' —
Sa'adda kuka kula da mai tufafi masu kyau nan, har kuka ce masa, “Idan ka yarda ka zauna a nan wuri mai kyau,'' mataulacin nan kuwa kuka ce masa, “Kai ka tsaya daga can,” ko kuwa, “Zauna a nan kasa a gaba na,”
4 ye did not judge fully in yourselves, and did become ill-reasoning judges.
Ashe ba kuna zartar da hukunci a tsakanin ku ba ke nan? Ba kun zama alkalai na mungayen tunani kenan ba?
5 Hearken, my brethren beloved, did not God choose the poor of this world, rich in faith, and heirs of the reign that He promised to those loving Him?
Ku saurara, ya 'yan'uwana kaunatattu, ashe, Allah bai zabi matalautan duniyar nan su zama mawadata cikin bangaskiya ba, su kuma zama magada a cikin mulkin nan da ya yi wa masu kaunar sa alkawari ba?
6 and ye did dishonour the poor one; do not the rich oppress you and themselves draw you to judgment-seats;
Amma, kun wulakanta matalauta! Ashe, ba masu arzikin ne suke matsa maku ba? Ba su ne kuwa suke jan ku zuwa gaban shari'a ba?
7 do they not themselves speak evil of the good name that was called upon you?
Ba kuma sune ke sabon sunan nan mai girma da ake kiran ku da shi ba?
8 If, indeed, royal law ye complete, according to the Writing, 'Thou shalt love thy neighbour as thyself,' — ye do well;
Duk da haka, idan kuka cika muhimmiyar shari'ar da nassi ya ce, “Ka kaunaci makwabcin ka kamar kanka,” to, madalla.
9 and if ye accept persons, sin ye do work, being convicted by the law as transgressors;
Amma in kun nuna bambanci, kun yi zunubi kenan, shari'a ta same ku da laifin keta umarni.
10 for whoever the whole law shall keep, and shall stumble in one [point], he hath become guilty of all;
Duk wanda yake kiyaye dukan shari'a, amma ya yi tuntube a hanya daya kadai, ya sabi shari'a gaba daya ke nan.
11 for He who is saying, 'Thou mayest not commit adultery,' said also, 'Thou mayest do no murder;' and if thou shalt not commit adultery, and shalt commit murder, thou hast become a transgressor of law;
Domin wanda ya ce, “Kada ka yi zina,” shi ne kuma ya ce, “Kada ka yi kisan kai.” Idan ba ka yi zina ba amma ka yi kisan kai, ai, ka zama mai taka shari'a kenan.
12 so speak ye and so do, as about by a law of liberty to be judged,
Saboda haka, ku yi magana ku kuma yi aiki kamar wadanda za a hukunta ta wurin 'yantacciyar shari'a.
13 for the judgment without kindness [is] to him not having done kindness, and exult doth kindness over judgment.
Gama hukunci yana zuwa ba tare da jinkai ba ga wadanda ba su nuna jinkai. Jinkai ya yi nasara a kan hukunci.
14 What [is] the profit, my brethren, if faith, any one may speak of having, and works he may not have? is that faith able to save him?
Ina amfanin haka, 'yan'uwana, idan wani ya ce yana da bangaskiya, kuma ba shi da ayyuka? Wannan bangaskiyar ba za ta cece shi ba, ko za ta iya?
15 and if a brother or sister may be naked, and may be destitute of the daily food,
Misali, idan wani dan'uwa ko 'yar'uwa ba su da tufa mai kyau ko suna rashin abincin yini.
16 and any one of you may say to them, 'Depart ye in peace, be warmed, and be filled,' and may not give to them the things needful for the body, what [is] the profit?
Misali, idan waninku kuma ya ce masu, “Ku tafi cikin salama, ku kasance da dumi ku koshi.” Idan baku ba su abubuwan da jiki ke bukata ba, ina amfanin wannnan?
17 so also the faith, if it may not have works, is dead by itself.
Haka ma, bangaskiya ita kadai, ba tare da aikin da ya nuna ta ba, matacciya ce.
18 But say may some one, Thou hast faith, and I have works, shew me thy faith out of thy works, and I will shew thee out of my works my faith:
To, wani zai ce, “Ai, kai kana da bangaskiya, ni kuwa ina da ayyuka.” Nuna mani bangaskiyar ka ba tare da ayyuka ba, ni kuma in nuna maka bangaskiya ta ta wurin ayyuka na.
19 thou — thou dost believe that God is one; thou dost well, and the demons believe, and they shudder!
Ka gaskanta cewa Allah daya ne; ka yi daidai. Amma ko aljannu ma sun gaskata, kuma suna rawar jiki.
20 And dost thou wish to know, O vain man, that the faith apart from the works is dead?
Kana so ka sani, kai marar azanci, cewa bangaskiya ba tare da ayyuka ba banza ce?
21 Abraham our father — was not he declared righteous out of works, having brought up Isaac his son upon the altar?
Ba an baratar da Ibrahim mahaifinmu ta wurin ayyuka ba, sa'adda ya mika Ishaku dansa a bisa bagadi?
22 dost thou see that the faith was working with his works, and out of the works the faith was perfected?
Ka gani, ashe, bangaskiyar sa ta yi aiki da ayyukan sa, kuma da cewa ta wurin ayyuka bangaskiyar sa ta ginu sosai.
23 and fulfilled was the Writing that is saying, 'And Abraham did believe God, and it was reckoned to him — to righteousness;' and, 'Friend of God' he was called.
Nassi kuma ya cika da ya ce, “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lisafta masa ita a matsayin adalci.” Aka kuma kira shi abokin Allah.
24 Ye see, then, that out of works is man declared righteous, and not out of faith only;
Kun ga, ta wurin ayyuka ne mutum yake samu baratarwa ba ta wurin bangaskiya kadai ba.
25 and in like manner also Rahab the harlot — was she not out of works declared righteous, having received the messengers, and by another way having sent forth?
Ta wannan hanyar kuma, ba Rahab karuwar nan ta samu baratarwa ta wurin ayyuka, da ta marabci masu leken asirin nan ta fitar da su ta wata hanya dabam ba?
26 for as the body apart from the spirit is dead, so also the faith apart from the works is dead.
Kamar yadda jiki idan ba tare da ruhu ba matacce ne, haka kuma, bangaskiya ba tare da ayyuka ba matacciya ce.