< Isaiah 22 >
1 The burden of the Valley of Vision. What — to thee, now, that thou hast gone up, All of thee — to the roofs?
Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
2 Full of stirs — a noisy city — an exulting city, Thy pierced are not pierced of the sword, Nor dead in battle.
Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
3 All thy rulers fled together from the bow, Bound have been all found of thee, They have been kept bound together, Afar off they have fled.
Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
4 Therefore I said, 'Look ye from me, I am bitter in my weeping, Haste not to comfort me, For the destruction of the daughter of my people.'
Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
5 For a day of noise, and of treading down, And of perplexity, [is] to the Lord, Jehovah of Hosts, In the valley of vision, digging down a wall, And crying unto the mountain.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
6 And Elam hath borne a quiver, In a chariot of men — horsemen, And Kir hath exposed a shield.
Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
7 And it cometh to pass, The choice of thy valleys have been full of chariots, And the horsemen place themselves diligently at the gate.
Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
8 And one removeth the covering of Judah, And thou lookest in that day Unto the armour of the house of the forest,
An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
9 And the breaches of the city of David ye have seen, For they have become many, And ye gather the waters of the lower pool,
kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
10 And the houses of Jerusalem ye did number, And ye break down the houses to fence the wall.
Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
11 And a ditch ye made between the two walls, For the waters of the old pool, And ye have not looked unto its Maker, And its Framer of old ye have not seen.
Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
12 And call doth the Lord, Jehovah of Hosts, In that day, to weeping and to lamentation, And to baldness and to girding on of sackcloth,
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
13 And lo, joy and gladness, slaying of oxen, And slaughtering of sheep, Eating of flesh, and drinking of wine, Eat and drink, for to-morrow we die.
Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
14 And revealed it hath been in mine ears, [By] Jehovah of Hosts: Not pardoned is this iniquity to you, Till ye die, said the Lord, Jehovah of Hosts.
Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
15 Thus said the Lord, Jehovah of Hosts: 'Go, enter in unto this steward, Unto Shebna, who [is] over the house:
Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
16 What — to thee here? And who — to thee here? That thou hast hewn out to thee here — a sepulchre? Hewing on high his sepulchre, Graving in a rock a dwelling for himself.
Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
17 Lo, Jehovah is casting thee up and down, A casting up and down, O mighty one,
“Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
18 And thy coverer covering, wrapping round, Wrappeth thee round, O babbler, On a land broad of sides — there thou diest, And there the chariots of thine honour [Are] the shame of the house of thy lord.
Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
19 And I have thrust thee from thy station, And from thine office he throweth thee down.
Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
20 And it hath come to pass, in that day, That I have called to my servant, To Eliakim son of Hilkiah.
“A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
21 And I have clothed him with thy coat, And with thy girdle I strengthen him, And thy garment I give into his hand, And he hath been for a father to the inhabitant of Jerusalem, And to the house of Judah.
Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
22 And I have placed the key Of the house of David on his shoulder, And he hath opened, and none is shutting, And hath shut, and none is opening.
Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
23 And I have fixed him a nail in a stedfast place, And he hath been for a throne of honour To the house of his father.
Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
24 And they have hanged on him All the honour of the house of his father, The offspring and the issue, All vessels of small quality, From vessels of basins to all vessels of flagons.
Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
25 In that day — an affirmation of Jehovah of Hosts, Moved is the nail that is fixed In a stedfast place, Yea, it hath been cut down, and hath fallen, And cut off hath been the burden that [is] on it, For Jehovah hath spoken!'
“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.