< Hosea 6 >
1 'Come, and we turn back unto Jehovah, For He hath torn, and He doth heal us, He doth smite, and He bindeth us up.
“Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
2 He doth revive us after two days, In the third day He doth raise us up, And we live before Him.
Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
3 And we know — we pursue to know Jehovah, As the dawn prepared is His going forth, And He cometh in as a shower to us, As gathered rain — sprinkling earth.'
Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
4 What do I do to thee, O Ephraim? What do I do to thee, O Judah? Your goodness [is] as a cloud of the morning, And as dew rising early — going.
“Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
5 Therefore I have hewed by prophets, I have slain them by sayings of My mouth, And My judgments to the light goeth forth.
Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
6 For kindness I desired, and not sacrifice, And a knowledge of God above burnt-offerings.
Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
7 And they, as Adam, transgressed a covenant, There they dealt treacherously against me.
Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
8 Gilead [is] a city of workers of iniquity, Slippery from blood.
Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
9 And as bands do wait for a man, A company of priests do murder — the way to Shechem, For wickedness they have done.
Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
10 In the house of Israel I have seen a horrible thing, There [is] the whoredom of Ephraim — defiled is Israel.
Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
11 Also, O Judah, appointed is a harvest to thee, In My turning back [to] the captivity of My people!
“Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,