< Hebrews 2 >
1 Because of this it behoveth [us] more abundantly to take heed to the things heard, lest we may glide aside,
Saboda haka, lalle ne mu kara mai da hankali musamman da abubuwan da mu ka ji, don kada mu yi sakaci, su sullube mana.
2 for if the word being spoken through messengers did become stedfast, and every transgression and disobedience did receive a just recompense,
Idan kuwa maganar nan da aka fada ta bakin mala'iku ta zama tabbatacciya, har kowanne keta umarni da rashin biyayya, suka gamu da sakamakonsu wanda ya kamace su,
3 how shall we escape, having neglected so great salvation? which a beginning receiving — to be spoken through the Lord — by those having heard was confirmed to us,
ta kaka za mu tsira, in mun ki kula da ceto mai girma haka? Domin Ubangiji da kansa, shi ne ya fara sanar da shi, wadanda suka saurare shi kuma suka tabbatar mana da shi.
4 God also bearing joint-witness both with signs and wonders, and manifold powers, and distributions of the Holy Spirit, according to His will.
San'nan kuma Allah da kansa ya shaida ta wasu alamu, da abubuwan al'ajabai, da mu'ajizai iri iri, da kuma baiwar Ruhu Mai Tsarki dabam dabam da ya rarraba kamar yadda ya nufa.
5 For not to messengers did He subject the coming world, concerning which we speak,
Ai ba ga mala'iku ba ne Allah ya sa mulkin duniyar nan da za a yi, wanda muke zance.
6 and one in a certain place did testify fully, saying, 'What is man, that Thou art mindful of him, or a son of man, that Thou dost look after him?
Amma wani ya shaida a wani wuri cewa, 'Mutum ma menene, har da za ka tuna da shi? Ko dan mutum ma, har da za ka kula da shi?'
7 Thou didst make him some little less than messengers, with glory and honour Thou didst crown him, and didst set him over the works of Thy hands,
Ka sa mutum ya gaza mala'iku; Ka nada shi da daukaka da girma. Bisa dukkan hallitta.
8 all things Thou didst put in subjection under his feet,' for in the subjecting to him the all things, nothing did He leave to him unsubjected, and now not yet do we see the all things subjected to him,
Ka dora shi a kan dukkan halittarka, ka kuma mallakar da kome a karkashin sawayensa. Domin Allah ya mallakar da dukkan abubuwa a karkashinsa. Bai bar kome a kebe ba. Amma kuwa har a yanzu ba mu ga yana sarrafa dukkan abubuwa ba tukuna.
9 and him who was made some little less than messengers we see — Jesus — because of the suffering of the death, with glory and honour having been crowned, that by the grace of God for every one he might taste of death.
Amma mun ga wani wanda dan lokaci aka sa shi ya gaza mala'iku, shine Yesu, an nada shi da daukaka da girma, saboda shan wuyarsa ta mutuwa, wanan kuwa duk ta wurin alherin Allah ne Yesu ya mutu saboda kowa.
10 For it was becoming to Him, because of whom [are] the all things, and through whom [are] the all things, many sons to glory bringing, the author of their salvation through sufferings to make perfect,
Saboda haka, ya dace ga Allah, shi da dukkan abubuwa suka kasance domin sa, ta gare shi, domin ya kawo 'ya'ya masu yawa ga samun daukaka. Domin a kammala cetonsu ta wurin shan wuyarsa.
11 for both he who is sanctifying and those sanctified [are] all of one, for which cause he is not ashamed to call them brethren,
Domin da shi mai tsarkakewar da kuma wadanda aka tsarkaken, duk tushensu daya ne. Saboda wanan dalili ne shi ya sa ba ya jin kunyar kiran su 'ya'uwansa.
12 saying, 'I will declare Thy name to my brethren, in the midst of an assembly I will sing praise to Thee;' and again, 'I will be trusting on Him;'
Da yace, ''zan sanar da sunanka ga ya'uwana, a tsakiyar taronsu zan yabe ka da waka.''
13 and again, 'Behold I and the children that God did give to me.'
Har wa yau, yace, ''Zan dogara a gare shi.'' Da kuma ''Ga ni nan, ni da 'ya'yan da Allah ya ba ni.''
14 Seeing, then, the children have partaken of flesh and blood, he himself also in like manner did take part of the same, that through death he might destroy him having the power of death — that is, the devil —
Wato tun da yake 'ya'yan Allah duk suna da nama da jini, Yesu ma ya dauki kamannin haka, ta wurin mutuwa ya hallakar da mai ikon mutuwa, wato Iblis.
15 and might deliver those, whoever, with fear of death, throughout all their life, were subjects of bondage,
Ya kuma 'yanta duk wadanda tun haihuwarsu suke zaman bauta sabo da tsoron mutuwa.
16 for, doubtless, of messengers it doth not lay hold, but of seed of Abraham it layeth hold,
Don hakika ba mala'iku yake taimako ba, a'a, zuriyar Ibrahim ne yake taimako.
17 wherefore it did behove him in all things to be made like to the brethren, that he might become a kind and stedfast chief-priest in the things with God, to make propitiation for the sins of the people,
Saboda haka, lalle ne ya zama kamar yan'uwansa ta kowacce hanya, domin ya zama babban Firist, mai jinkai, mai aminci kuma na al'amarin Allah, ya kuma mika hadayar sulhu ta gafarta zunuban jama'a.
18 for in that he suffered, himself being tempted, he is able to help those who are tempted.
Tun da yake Yesu ma da kansa ya sha wahala, sa'adda aka gwada shi, don haka, zai taimaki wadanda ake yi wa gwaji.