< Genesis 36 >

1 And these [are] births of Esau, who [is] Edom.
Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
2 Esau hath taken his wives from the daughters of Canaan: Adah daughter of Elon the Hittite, and Aholibamah daughter of Anah, daughter of Zibeon the Hivite,
Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
3 and Bashemath daughter of Ishmael, sister of Nebajoth.
ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
4 And Adah beareth to Esau, Eliphaz; and Bashemath hath born Reuel;
Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
5 and Aholibamah hath born Jeush, and Jaalam, and Korah. These [are] sons of Esau, who were born to him in the land of Canaan.
Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
6 And Esau taketh his wives, and his sons, and his daughters, and all the persons of his house, and his cattle, and all his beasts, and all his substance which he hath acquired in the land of Canaan, and goeth into the country from the face of Jacob his brother;
Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
7 for their substance was more abundant than to dwell together, and the land of their sojournings was not able to bear them because of their cattle;
Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
8 and Esau dwelleth in mount Seir: Esau is Edom.
Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
9 And these [are] births of Esau, father of Edom, in mount Seir.
Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
10 These [are] the names of the sons of Esau: Eliphaz son of Adah, wife of Esau; Reuel son of Bashemath, wife of Esau.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
11 And the sons of Eliphaz are Teman, Omar, Zepho, and Gatam, and Kenaz;
’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
12 and Timnath hath been concubine to Eliphaz son of Esau, and she beareth to Eliphaz, Amalek; these [are] sons of Adah wife of Esau.
Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
13 And these [are] sons of Reuel: Nahath and Zerah, Shammah and Mizzah; these were sons of Bashemath wife of Esau.
’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
14 And these have been the sons of Aholibamah daughter of Anah, daughter of Zibeon, wife of Esau; and she beareth to Esau, Jeush and Jaalam and Korah.
’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
15 These [are] chiefs of the sons of Esau: sons of Eliphaz, first-born of Esau: chief Teman, chief Omar, chief Zepho, chief Kenaz,
Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
16 chief Korah, chief Gatam, chief Amalek; these [are] chiefs of Eliphaz, in the land of Edom; these [are] sons of Adah.
Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
17 And these [are] sons of Reuel son of Esau: chief Nahath, chief Zerah, chief Shammah, chief Mizzah; these [are] chiefs of Reuel, in the land of Edom; these [are] sons of Bashemath wife of Esau.
’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
18 And these [are] sons of Aholibamah wife of Esau: chief Jeush, chief Jaalam, chief Korah; these [are] chiefs of Aholibamah daughter of Anah, wife of Esau.
’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
19 These [are] sons of Esau (who [is] Edom), and these their chiefs.
Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
20 These [are] sons of Seir the Horite, the inhabitants of the land: Lotan, and Shobal, and Zibeon, and Anah,
Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
21 and Dishon, and Ezer, and Dishan; these [are] chiefs of the Horites, sons of Seir, in the land of Edom.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
22 And the sons of Lotan are Hori and Heman; and a sister of Lotan [is] Timna.
’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
23 And these [are] sons of Shobal: Alvan and Manahath, and Ebal, Shepho and Onam.
’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
24 And these [are] sons of Zibeon, both Ajah and Anah: it [is] Anah that hath found the Imim in the wilderness, in his feeding the asses of Zibeon his father.
’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
25 And these [are] sons of Anah: Dishon, and Aholibamah daughter of Anah.
’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
26 And these [are] sons of Dishon: Hemdan, and Eshban, and Ithran, and Cheran.
’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
27 These [are] sons of Ezer: Bilhan, and Zaavan, and Akan.
’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
28 These [are] sons of Dishan: Uz and Aran.
’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
29 These [are] chiefs of the Horite: chief Lotan, chief Shobal, chief Zibeon, chief Anah,
Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
30 chief Dishon, chief Ezer, chief Dishan: these [are] chiefs of the Horite in reference to their chiefs in the land of Seir.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
31 And these [are] the kings who have reigned in the land of Edom before the reigning of a king over the sons of Israel.
Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
32 And Bela son of Beor reigneth in Edom, and the name of his city [is] Dinhabah;
Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
33 and Bela dieth, and reign in his stead doth Jobab son of Zerah from Bozrah;
Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
34 and Jobab dieth, and reign in his stead doth Husham from the land of the Temanite.
Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
35 And Husham dieth, and reign in his stead doth Hadad son of Bedad (who smiteth Midian in the field of Moab), and the name of his city [is] Avith;
Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
36 and Hadad dieth, and reign in his stead doth Samlah of Masrekah;
Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
37 and Samlah dieth, and reign in his stead doth Saul from Rehoboth of the River;
Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
38 and Saul dieth, and reign in his stead doth Baal-hanan son of Achbor;
Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
39 and Baal-hanan son of Achbor dieth, and reign in his stead doth Hadar, and the name of his city [is] Pau; and his wife's name [is] Mehetabel daughter of Matred, daughter of Me-zahab.
Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
40 And these [are] the names of the chiefs of Esau, according to their families, according to their places, by their names: chief Timnah, chief Alvah, chief Jetheth,
Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
41 chief Aholibamah, chief Elah, chief Pinon,
Oholibama, Ela, Finon.
42 chief Kenaz, chief Teman, chief Mibzar,
Kenaz, Teman, Mibzar.
43 chief Magdiel, chief Iram: these [are] chiefs of Edom, in reference to their dwellings, in the land of their possession; he [is] Esau father of Edom.
Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.

< Genesis 36 >