< Genesis 30 >

1 And Rachel seeth that she hath not borne to Jacob, and Rachel is envious of her sister, and saith unto Jacob, 'Give me sons, and if there is none — I die.'
Sa’ad da Rahila ta ga cewa ba tă haifa wa Yaƙub’ya’ya ba, sai ta fara kishin’yar’uwarta. Saboda haka ta ce wa Yaƙub, “Ka ba ni’ya’ya, ko kuwa in mutu!”
2 And Jacob's anger burneth against Rachel, and he saith, 'Am I in stead of God who hath withheld from thee the fruit of the womb?'
Yaƙub ya fusata da ita ya ce, “Ina a matsayin Allah ne wanda ya hana ke samun’ya’ya?”
3 And she saith, 'Lo, my handmaid Bilhah, go in unto her, and she doth bear on my knees, and I am built up, even I, from her;'
Sa’an nan ta ce, “Ga Bilha, mai baiwata, ka kwana da ita don tă haifa mini’ya’ya, ta gare ta kuwa ni ma in gina iyali.”
4 and she giveth to him Bilhah her maid-servant for a wife, and Jacob goeth in unto her;
Saboda haka ta ba shi baranyarta Bilha tă zama matarsa. Yaƙub kuwa ya kwana da ita,
5 and Bilhah conceiveth, and beareth to Jacob a son,
ta kuwa yi ciki, ta kuma haifi ɗa.
6 and Rachel saith, 'God hath decided for me, and also hath hearkened to my voice, and giveth to me a son;' therefore hath she called his name Dan.
Sa’an nan Rahila ta ce, “Allah ya baratar da ni; ya saurari roƙona ya kuma ba ni ɗa.” Saboda wannan ta ba shi suna Dan.
7 And Bilhah, Rachel's maid-servant, conceiveth again, and beareth a second son to Jacob,
Baranyar Rahila ta sāke yin ciki ta kuma haifi wa Yaƙub ɗa na biyu.
8 and Rachel saith, 'With wrestlings of God I have wrestled with my sister, yea, I have prevailed;' and she calleth his name Napthali.
Sai Rahila ta ce, “Na yi kokawa sosai da’yar’uwata, na kuwa yi nasara.” Saboda haka ta kira shi Naftali.
9 And Leah seeth that she hath ceased from bearing, and she taketh Zilpah her maid-servant, and giveth her to Jacob for a wife;
Sa’ad da Liyatu ta ga cewa ta daina haihuwa, sai ta ɗauki mai hidimarta Zilfa ta ba da ita ga Yaƙub tă zama matarsa.
10 and Zilpah, Leah's maid-servant, beareth to Jacob a son,
Baranyar Liyatu, Zilfa ta haifa wa Yaƙub ɗa.
11 and Leah saith, 'A troop is coming;' and she calleth his name Gad.
Sai Liyatu ta ce, “Na yi sa’a!” Saboda haka ta ba shi suna Gad.
12 And Zilpah, Leah's maid-servant, beareth a second son to Jacob,
Zilfa baranyar Liyatu ta haifa wa Yaƙub ɗa na biyu.
13 and Leah saith, 'Because of my happiness, for daughters have pronounced me happy;' and she calleth his name Asher.
Sai Liyatu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Mata za su ce da ni mai farin ciki.” Saboda haka ta sa masa suna Asher.
14 And Reuben goeth in the days of wheat-harvest, and findeth love-apples in the field, and bringeth them in unto Leah, his mother, and Rachel saith unto Leah, 'Give to me, I pray thee, of the love-apples of thy son.'
A lokacin girbin alkama, sai Ruben ya je jeji ya ɗebo manta-uwa ya kawo wa mahaifiyarsa Liyatu. Sai Rahila ta ce wa Liyatu, “Ina roƙonki ki ɗan sam mini manta-uwa ɗanki.”
15 And she saith to her, 'Is thy taking my husband a little thing, that thou hast taken also the love-apples of my son?' and Rachel saith, 'Therefore doth he lie with thee to-night, for thy son's love-apples.'
Amma ta ce mata, “Bai ishe ki ba ne da kika ƙwace mijina? Yanzu kuma kina so ki ƙwace manta-uwa na yarona?” Sai Rahila ta ce “Shi ke nan, mijina zai iya kwana da ke yau saboda manta-uwa na ɗanki.”
16 And Jacob cometh in from the field at evening; and Leah goeth to meet him, and saith, 'Unto me dost thou come in, for hiring I have hired thee with my son's love-apples;' and he lieth with her during that night.
Saboda haka sa’ad da Yaƙub ya dawo daga jeji a wannan yamma sai Liyatu ta fito ta tarye shi. Ta ce, “Dole ka kwana da ni, na yi hayarka da manta-uwa na ɗana.” Saboda haka ya kwana da ita a wannan dare.
17 And God hearkeneth unto Leah, and she conceiveth, and beareth to Jacob a son, a fifth,
Allah ya saurari Liyatu, ta kuwa yi ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na biyar.
18 and Leah saith, 'God hath given my hire, because I have given my maid-servant to my husband;' and she calleth his name Issachar.
Sai Liyatu ta ce, “Allah ya sāka mini saboda na ba da mai hidimata ga mijina.” Saboda haka ta ba shi suna Issakar.
19 And conceive again doth Leah, and she beareth a sixth son to Jacob,
Liyatu ta sāke yin ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na shida.
20 and Leah saith, 'God hath endowed me — a good dowry; this time doth my husband dwell with me, for I have borne to him six sons;' and she calleth his name Zebulun;
Sai Liyatu ta ce, “Allah ya ba ni kyauta mai daraja. A wannan lokaci mijina zai darajarta ni, domin na haifa masa’ya’ya maza shida.” Saboda haka ta ba shi suna Zebulun.
21 and afterwards hath she born a daughter, and calleth her name Dinah.
Daga baya ta haifi’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
22 And God remembereth Rachel, and God hearkeneth unto her, and openeth her womb,
Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.
23 and she conceiveth and beareth a son, and saith, 'God hath gathered up my reproach;'
Sai ta yi ciki ta kuma haifi ɗa ta ce, “Allah ya ɗauke mini kunyata.”
24 and she calleth his name Joseph, saying, 'Jehovah is adding to me another son.'
Ta ba shi suna Yusuf, ta kuma ce, “Bari Ubangiji yă ƙara mini wani ɗa.”
25 And it cometh to pass, when Rachel hath borne Joseph, that Jacob saith unto Laban, 'Send me away, and I go unto my place, and to my land;
Bayan Rahila ta haifi Yusuf, sai Yaƙub ya ce wa Laban, “Ka sallame ni don in koma ƙasata.
26 give up my wives and my children, for whom I have served thee, and I go; for thou — thou hast known my service which I have served thee.'
Ba ni matana da’ya’yana, waɗanda na bauta maka dominsu, zan kuwa tafi. Ka dai san yadda na bauta maka.”
27 And Laban saith unto him, 'If, I pray thee, I have found grace in thine eyes — I have observed diligently that Jehovah doth bless me for thy sake.'
Amma Laban ya ce masa, “In na sami tagomashi daga gare ka, ina roƙonka ka zauna. Na gane ta wurin duba cewaUbangiji ya albarkace ni saboda kai.”
28 He saith also, 'Define thy hire to me, and I give.'
Ya ƙara da cewa, “Faɗa albashinka, zan kuwa biya shi.”
29 And he saith unto him, 'Thou — thou hast known that which I have served thee [in], and that which thy substance was with me;
Yaƙub ya ce masa, “Ka dai san yadda na yi maka aiki da kuma yadda dabbobinka suka yi yawa a hannuna.
30 for [it is] little which thou hast had at my appearance, and it breaketh forth into a multitude, and Jehovah blesseth thee at my coming; and now, when do I make, I also, for mine own house?'
Kaɗan da kake da shi kafin zuwata ya ƙaru sosai, kuma Ubangiji ya albarkace ka a duk inda na tafi. Amma yanzu, yaushe zan yi wani abu domin gidana ni ma?”
31 And he saith, 'What do I give to thee?' And Jacob saith, 'Thou dost not give me anything; if thou do for me this thing, I turn back; I have delight; thy flock I watch;
Sai Laban ya yi tambaya, “Me zan ba ka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Kada ka ba ni wani abu. Amma in za ka yi mini abu guda ɗaya, zan ci gaba da kiwon garkunanka, ina kuma lura da su.
32 I pass through all thy flock to-day to turn aside from thence every sheep speckled and spotted, and every brown sheep among the lambs, and speckled and spotted among the goats — and it hath been my hire;
Bari in ratsa cikin dukan garkunanka yau in fid da masu dabbare-dabbare da tumaki babare-babare, da kowane ɗan rago baƙi, da dabbare-dabbare da babare-babare na awaki daga ciki, waɗannan ne za su zama ladana.
33 and my righteousness hath answered for me in the day to come, when it cometh in for my hire before thy face; — every one which is not speckled and spotted among [my] goats, and brown among [my] lambs — it is stolen with me.'
Gaskiyata kuwa za tă zama mini shaida nan gaba, duk sa’ad da ka bincika a kan albashin da ka biya ni. Duk akuyar da take tawa da ba dabbare-dabbare ko babare-babare, ko ɗan ragon da ba baƙi ba, zai kasance sata na yi.”
34 And Laban saith, 'Lo, O that it were according to thy word;'
Sai Laban ya ce, “Na yarda. Bari yă zama yadda ka faɗa.”
35 and he turneth aside during that day the ring-streaked and the spotted he-goats, and all the speckled and the spotted she-goats, every one that [hath] white in it, and every brown one among the lambs, and he giveth into the hand of his sons,
A wannan rana ya ware dukan bunsurai da suke dabbare-dabbare da masu zāne-zāne, da dukan awakin da suke dabbare-dabbare (duka da suke da fari-fari a jikinsu), da dukan baƙaƙen tumaki, ya sa su a hannun’ya’yansa maza.
36 and setteth a journey of three days between himself and Jacob; and Jacob is feeding the rest of the flock of Laban.
Sa’an nan ya sa nisan tafiya kwana uku tsakaninsa da Yaƙub, yayinda Yaƙub ya ci gaba da lura da sauran garkunan Laban Yaƙub.
37 And Jacob taketh to himself a rod of fresh poplar, and of the hazel and chesnut, and doth peel in them white peelings, making bare the white that [is] on the rods,
Yaƙub ya samo ɗanyen reshen itatuwan aduruku, da na katambiri, da na durumi, ya ɓare ya bar fararen cikin katakon rassan.
38 and setteth up the rods which he hath peeled in the gutters in the watering troughs (when the flock cometh in to drink), over-against the flock, that they may conceive in their coming in to drink;
Sa’an nan ya zuba ɓararre rassan cikin dukan kwamame na banruwa saboda su kasance a gaban garkunan sa’ad da suka zo shan ruwa. A sa’ad da garkunan suke barbara suka kuma zo shan ruwa,
39 and the flocks conceive at the rods, and the flock beareth ring-streaked, speckled, and spotted ones.
sai su yi barbara a gaban rassan. Sai kuwa su haifi ƙanana masu zāne dabbare-dabbare, ko babare-babare ko masu zāne-zāne.
40 And the lambs hath Jacob parted, and he putteth the face of the flock towards the ring-streaked, also all the brown in the flock of Laban, and he setteth his own droves by themselves, and hath not set them near Laban's flock.
Sai Yaƙub yă ware ƙananan garken dabam, amma sai yă sa sauran su fuskanci dabbobin da suke dabbare-dabbare da kuma baƙaƙe da suke na Laban. Ta haka ya ware garkuna dabam domin kansa bai kuwa haɗa su da dabbobin Laban ba.
41 And it hath come to pass whenever the strong ones of the flock conceive, that Jacob set the rods before the eyes of the flock in the gutters, to cause them to conceive by the rods,
A duk sa’ad da ƙarfafa dabbobi mata suke barbara, Yaƙub yakan zuba rassan a kwamame a gaban dabbobin saboda su yi barbara kusa da rassan,
42 and when the flock is feeble, he doth not set [them]; and the feeble ones have been Laban's, and the strong ones Jacob's.
amma in dabbobin raunana ne, ba ya sa su a can. Saboda haka raunanan dabbobi suka zama na Laban, ƙarfafan kuma suka zama na Yaƙub.
43 And the man increaseth very exceedingly, and hath many flocks, and maid-servants, and men-servants, and camels, and asses.
Ta haka mutumin ya zama riƙaƙƙe mai arziki, ya kasance mai manya-manyan garkuna, da bayi mata da maza, da raƙuma da kuma jakuna.

< Genesis 30 >