< Genesis 29 >
1 And Jacob lifteth up his feet, and goeth towards the land of the sons of the east;
Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
2 and he looketh, and lo, a well in the field, and lo, there three droves of a flock crouching by it, for from that well they water the droves, and the great stone [is] on the mouth of the well.
A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
3 (When thither have all the droves been gathered, and they have rolled the stone from off the mouth of the well, and have watered the flock, then they have turned back the stone on the mouth of the well to its place.)
Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
4 And Jacob saith to them, 'My brethren, from whence [are] ye?' and they say, 'We [are] from Haran.'
Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
5 And he saith to them, 'Have ye known Laban, son of Nahor?' and they say, 'We have known.'
Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
6 And he saith to them, 'Hath he peace?' and they say, 'Peace; and lo, Rachel his daughter is coming with the flock.'
Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
7 And he saith, 'Lo, the day [is] still great, [it is] not time for the cattle to be gathered; water ye the flock, and go, delight yourselves.'
Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
8 And they say, 'We are not able, till that all the droves be gathered together, and they have rolled away the stone from the mouth of the well, and we have watered the flock.'
Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
9 He is yet speaking with them, and Rachel hath come with the flock which her father hath, for she [is] shepherdess;
Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
10 and it cometh to pass when Jacob hath seen Rachel, daughter of Laban his mother's brother, and the flock of Laban his mother's brother, that Jacob cometh nigh and rolleth the stone from off the mouth of the well, and watereth the flock of Laban his mother's brother.
Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
11 And Jacob kisseth Rachel, and lifteth up his voice, and weepeth,
Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
12 and Jacob declareth to Rachel that he [is] her father's brother, and that he [is] Rebekah's son, and she runneth and declareth to her father.
Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
13 And it cometh to pass, when Laban heareth the report of Jacob his sister's son, that he runneth to meet him, and embraceth him, and kisseth him, and bringeth him in unto his house; and he recounteth to Laban all these things,
Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
14 and Laban saith to him, 'Only my bone and my flesh [art] thou;' and he dwelleth with him a month of days.
Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
15 And Laban saith to Jacob, 'Is it because thou [art] my brother that thou hast served me for nought? declare to me what [is] thy hire.'
sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
16 And Laban hath two daughters, the name of the elder [is] Leah, and the name of the younger Rachel,
Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
17 and the eyes of Leah [are] tender, and Rachel hath been fair of form and fair of appearance.
Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
18 And Jacob loveth Rachel, and saith, 'I serve thee seven years for Rachel thy younger daughter:'
Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
19 and Laban saith, 'It is better for me to give her to thee than to give her to another man; dwell with me;'
Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
20 and Jacob serveth for Rachel seven years; and they are in his eyes as some days, because of his loving her.
Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
21 And Jacob saith unto Laban, 'Give up my wife, for my days have been fulfilled, and I go in unto her;'
Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
22 and Laban gathereth all the men of the place, and maketh a banquet.
Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
23 And it cometh to pass in the evening, that he taketh Leah, his daughter, and bringeth her in unto him, and he goeth in unto her;
Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
24 and Laban giveth to her Zilpah, his maid-servant, to Leah his daughter, a maid-servant.
Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
25 And it cometh to pass in the morning, that lo, it [is] Leah; and he saith unto Laban, 'What [is] this thou hast done to me? for Rachel have I not served with thee? and why hast thou deceived me?'
Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
26 And Laban saith, 'It is not done so in our place, to give the younger before the first-born;
Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
27 fulfil the week of this one, and we give to thee also this one, for the service which thou dost serve with me yet seven other years.'
Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
28 And Jacob doth so, and fulfilleth the week of this one, and he giveth to him Rachel his daughter, to him for a wife;
Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
29 and Laban giveth to Rachel his daughter Bilhah his maid-servant, for a maid-servant to her.
Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
30 And he goeth in also unto Rachel, and he also loveth Rachel more than Leah; and he serveth with him yet seven other years.
Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
31 And Jehovah seeth that Leah [is] the hated one, and He openeth her womb, and Rachel [is] barren;
Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
32 and Leah conceiveth, and beareth a son, and calleth his name Reuben, for she said, 'Because Jehovah hath looked on mine affliction; because now doth my husband love me.'
Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
33 And she conceiveth again, and beareth a son, and saith, 'Because Jehovah hath heard that I [am] the hated one, He also giveth to me even this [one];' and she calleth his name Simeon.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
34 And she conceiveth again, and beareth a son, and saith, 'Now [is] the time, my husband is joined unto me, because I have born to him three sons,' therefore hath [one] called his name Levi.
Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
35 And she conceiveth again, and beareth a son, and saith this time, 'I praise Jehovah;' therefore hath she called his name Judah; and she ceaseth from bearing.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.