< Genesis 26 >

1 And there is a famine in the land, besides the first famine which was in the days of Abraham, and Isaac goeth unto Abimelech king of the Philistines, to Gerar.
Aka yi yunwa a ƙasar; ban da yunwar da aka yi da fari a zamanin Ibrahim, sai Ishaku ya tafi wurin Abimelek sarkin Filistiyawa a Gerar.
2 And Jehovah appeareth unto him, and saith, 'Go not down towards Egypt, tabernacle in the land concerning which I speak unto thee,
Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ishaku ya ce, “Kada ka gangara zuwa Masar; ka yi zauna a ƙasar da zan faɗa maka.
3 sojourn in this land, and I am with thee, and bless thee, for to thee and to thy seed I give all these lands, and I have established the oath which I have sworn to Abraham thy father;
Ka zauna a wannan ƙasa na ɗan lokaci, zan kuwa kasance tare da kai, zan kuma albarkace ka. Gama zan ba da waɗannan ƙasashe gare ka da kuma zuriyarka. Zan kuma cika rantsuwar da na yi wa mahaifinka Ibrahim.
4 and I have multiplied thy seed as stars of the heavens, and I have given to thy seed all these lands; and blessed themselves in thy seed have all nations of the earth;
Zan sa zuriyarka ta yi yawa kamar taurari a sararin sama zan kuwa ba su dukan waɗannan ƙasashe, ta wurin’ya’yanka kuma za a albarkaci dukan al’umman duniya,
5 because that Abraham hath hearkened to My voice, and keepeth My charge, My commands, My statutes, and My laws.'
domin Ibrahim ya yi mini biyayya ya kuma kiyaye umarnaina, ƙa’idodina da kuma dokokina.”
6 And Isaac dwelleth in Gerar;
Sai Ishaku ya zauna a Gerar.
7 and men of the place ask him of his wife, and he saith, 'She [is] my sister:' for he hath been afraid to say, 'My wife — lest the men of the place kill me for Rebekah, for she [is] of good appearance.'
Sa’ad da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, “’Yar’uwata ce,” gama yana tsoro yă ce, “Ita matata ce.” Ya yi tunani, “Mutane wannan wuri za su kashe ni ta dalili Rebeka, domin kyakkyawa ce.”
8 And it cometh to pass, when the days have been prolonged to him there, that Abimelech king of the Philistines looketh through the window, and seeth, and lo, Isaac is playing with Rebekah his wife.
Sa’ad da Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba daga taga ya ga Ishaku yana rungumar matarsa Rebeka.
9 And Abimelech calleth for Isaac, and saith, 'Lo, she [is] surely thy wife; and how hast thou said, She [is] my sister?' and Isaac saith unto him, 'Because I said, Lest I die for her.'
Saboda haka Abimelek ya aika Ishaku yă je, sa’an nan ya ce, “Tabbatacce ita matarka ce! Me ya sa ka ce, ‘Ita’yar’uwata ce?’” Ishaku ya amsa masa ya ce, “Don na yi tsammani zan rasa raina saboda ita.”
10 And Abimelech saith, 'What [is] this thou hast done to us? as a little thing one of the people had lain with thy wife, and thou hadst brought upon us guilt;'
Sa’an nan Abimelek ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Da a ce wani daga mazanmu ya kwana da matarka, ai, da ka jawo laifi a kanmu.”
11 and Abimelech commandeth all the people, saying, 'He who cometh against this man or against his wife, dying doth die.'
Saboda haka Abimelek ya yi umarni ga dukan mutane. “Duk wanda ya fitine wannan mutum ko matarsa, tabbatacce za a kashe shi.”
12 And Isaac soweth in that land, and findeth in that year a hundredfold, and Jehovah blesseth him;
Ishaku ya shuka hatsi a wannan ƙasa, a shekaran nan ya yi girbi ninki ɗari, domin Ubangiji ya albarkace shi.
13 and the man is great, and goeth on, going on and becoming great, till that he hath been very great,
Mutumin ya arzuta, arzikinsa ya yi ta haɓaka har ya zama attajiri.
14 and he hath possession of a flock, and possession of a herd, and an abundant service; and the Philistines envy him,
Ya kasance da garkunan tumaki da na shanu da bayi masu yawa, har Filistiyawa suka yi ƙyashinsa.
15 and all the wells which his father's servants digged in the days of Abraham his father, the Philistines have stopped them, and fill them with dust.
Saboda haka dukan rijiyoyin da bayin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin da mahaifinsa Ibrahim yake da rai, Filistiyawa sun toshe su, suka kuma ciccike su da ƙasa.
16 And Abimelech saith unto Isaac, 'Go from us; for thou hast become much mightier than we;'
Sai Abimelek ya ce wa Ishaku, “Fita daga cikinmu; ka fi ƙarfinmu.”
17 and Isaac goeth from thence, and encampeth in the valley of Gerar, and dwelleth there;
Saboda haka Ishaku ya fita daga can, ya yi sansani a Kwarin Gerar, ya kuma zauna a can.
18 and Isaac turneth back, and diggeth the wells of water which they digged in the days of Abraham his father, which the Philistines do stop after the death of Abraham, and he calleth to them names according to the names which his father called them.
Ishaku ya sāke tona rijiyoyi waɗanda dā aka haƙa a zamanin Ibrahim mahaifinsa, gama Filistiyawa suka tattoshe bayan mutuwar Ibrahim, ya kuma sa musu sunayen da mahaifinsa ya ba su.
19 And Isaac's servants dig in the valley, and find there a well of living water,
Barorin Ishaku suka haƙa cikin kwarin suka kuwa sami rijiya mai ruwa mai kyau a can.
20 and shepherds of Gerar strive with shepherds of Isaac, saying, 'The water [is] ours;' and he calleth the name of the well 'Strife,' because they have striven habitually with him;
Amma makiyayan Gerar suka yi faɗa da na Ishaku suka ce, “Ruwan namu ne!” Saboda haka Ishaku ya ba wa rijiyar suna Esek, domin sun yi faɗa da shi.
21 and they dig another well, and they strive also for it, and he calleth its name 'Hatred.'
Sai suka haƙa wata rijiya, amma suka yi faɗa a kanta ita ma, saboda haka ya ce da ita Sitna.
22 And he removeth from thence, and diggeth another well, and they have not striven for it, and he calleth its name Enlargements, and saith, 'For — now hath Jehovah given enlargement to us, and we have been fruitful in the land.'
Sai Ishaku ya matsa daga can ya sāke haƙa wata rijiyar, babu wani kuma da yi faɗa a kanta. Sai ya ba ta suna Rehobot, yana cewa, “Yanzu Ubangiji ya ba mu wuri, za mu kuwa yi ta haihuwa a ƙasar.”
23 And he goeth up from thence [to] Beer-Sheba,
Daga can ya haura zuwa Beyersheba.
24 and Jehovah appeareth unto him during that night, and saith, 'I [am] the God of Abraham thy father, fear not, for I [am] with thee, and have blessed thee, and have multiplied thy seed, because of Abraham My servant;'
A wannan dare Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka Ibrahim. Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan albarkace ka, zan kuma ƙara yawan zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”
25 and he buildeth there an altar, and preacheth in the name of Jehovah, and stretcheth out there his tent, and there Isaac's servants dig a well.
Sai Ishaku ya gina bagade a can, ya kuma kira bisa sunan Ubangiji. A can ya kafa tentinsa, a can kuma bayinsa suka haƙa wata rijiya.
26 And Abimelech hath gone unto him from Gerar, and Ahuzzath his friend, and Phichol head of his host;
Ana cikin haka, sai Abimelek ya zo wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzzat mai ba shi shawara da Fikol shugaban mayaƙansa.
27 and Isaac saith unto them, 'Wherefore have ye come unto me, and ye have hated me, and ye send me away from you?'
Ishaku ya tambaye su, “Me ya kawo ku gare ni, da yake kun yi gāba da ni, kuka kuma kore ni?”
28 And they say, 'We have certainly seen that Jehovah hath been with thee, and we say, 'Let there be, we pray thee, an oath between us, between us and thee, and let us make a covenant with thee;
Suka amsa, “Mun ga a zahiri cewa Ubangiji yana tare da kai; saboda haka muka ce, ‘Dole rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai.’ Bari mu yi yarjejjeniya da kai
29 do not evil with us, as we have not touched thee, and as we have only done good with thee, and send thee away in peace; thou [art] now blessed of Jehovah.'
cewa ba za ka cuce mu ba, kamar yadda ba mu fitine ka ba, amma muka yi maka kirki, muka kuma sallame ka cikin salama. Yanzu kuwa kai albarkatacce ne na Ubangiji.”
30 And he maketh for them a banquet, and they eat and drink,
Sai Ishaku ya shirya musu liyafa, suka ci suka kuma sha.
31 and rise early in the morning, and swear one to another, and Isaac sendeth them away, and they go from him in peace.
Kashegari da sassafe sai mutanen suka yi wa juna rantsuwa. Sa’an nan Ishaku ya sallame su, suka kuwa tafi cikin salama.
32 And it cometh to pass during that day that Isaac's servants come and declare to him concerning the circumstances of the well which they have digged, and say to him, 'We have found water;'
A wannan rana bayin Ishaku suka zo suka faɗa masa game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, “Mun sami ruwa!”
33 and he calleth it Shebah, [oath, ] therefore the name of the city [is] Beer-Sheba, [well of the oath, ] unto this day.
Sai ya kira ta Shiba, don haka har wa yau ana kira garin Beyersheba.
34 And Esau is a son of forty years, and he taketh a wife, Judith, daughter of Beeri the Hittite, and Bashemath, daughter of Elon the Hittite,
Sa’ad da Yaƙub ya kai shekaru arba’in da haihuwa, sai ya auri Yudit’yar Beyeri mutumin Hitti, da kuma Basemat’yar Elon mutumin Hitti.
35 and they are a bitterness of spirit to Isaac and to Rebekah.
Su ne suka zama sanadin baƙin ciki ga Ishaku da Rebeka.

< Genesis 26 >