< Galatians 4 >
1 And I say, so long time as the heir is a babe, he differeth nothing from a servant — being lord of all,
Ina cewa muddin magaji yaro ne, babu bambancin sa da bawa, ko da yake shine mai mallakan dukan kadarorin.
2 but is under tutors and stewards till the time appointed of the father,
A maimakon haka, yana karkashin masu jagora da amintattu har sai lokacin da mahaifinsa ya ajiye.
3 so also we, when we were babes, under the elements of the world were in servitude,
Hakannan mu ma, lokaci da muke yara, an rike mu cikin kangi na tushin ka'idojin wannan duniya.
4 and when the fulness of time did come, God sent forth His Son, come of a woman, come under law,
Amma da lokacin ya yi daidai, Allah ya aiko da dansa, haihuwar mace, haihuwar karkashin shari'a.
5 that those under law he may redeem, that the adoption of sons we may receive;
Ya yi haka ne domin ya fanshi wadanda ke a karkashin shari'a, domin mu karbi diyanci a matsayin 'ya'ya.
6 and because ye are sons, God did send forth the spirit of His Son into your hearts, crying, 'Abba, Father!'
Domin ku 'ya'ya ne, Allah ya aiko da Ruhun Dansa cikin zuciyarmu, Ruhun wanda ke kirar, “Abba, Uba.”
7 so that thou art no more a servant, but a son, and if a son, also an heir of God through Christ.
Saboda wannan dalilin kai ba kuma bawa ba ne amma da. Idan kai da ne, hakannan kuma kai ma magaji ne ta wurin Allah.
8 But then, indeed, not having known God, ye were in servitude to those not by nature gods,
Duk da haka a da, da ba ku san Allah ba, bayi ne ku ga alloli wadanda ainihi ba alloli ba ne ko kadan.
9 and now, having known God — and rather being known by God — how turn ye again unto the weak and poor elements to which anew ye desire to be in servitude?
Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma, yanzu da Allah ya san ku, me ya sa kuke sake komawa zuwa ga tushen ka'idodin nan mara karfi da amfani? Kuna so ku sake komawa zaman bayi kuma daga farko?
10 days ye observe, and months, and times, and years!
Kuna kiyaye ranaku na musamman, sabobin watanni, lokatai, da shekaru.
11 I am afraid of you, lest in vain I did labour toward you.
Ina ji maku tsoro. Ina tsoro cewa kamar na yi aiki cikinku a wofi.
12 Become as I [am] — because I also [am] as ye brethren, I beseech you; to me ye did no hurt,
Ina rokon ku 'yan'uwa, ku zama kamar yadda nake, domin ni ma na zama kamar ku. Ba ku yi mani laifin komai ba.
13 and ye have known that through infirmity of the flesh I did proclaim good news to you at the first,
Amma kun sani cewa saboda rashin lafiya ne na yi maku shelar bishara da farko.
14 and my trial that [is] in my flesh ye did not despise nor reject, but as a messenger of God ye did receive me — as Christ Jesus;
Ko da yake halin da nake ciki cikin jiki a zahiri ya sa ku cikin gwaji, ba ku raina ni ba ko kuma kuka watsar da ni. A maimakon haka, kun karbe ni kamar mala'ikan Allah, kamar ni Almasihu Yesu ne da kansa.
15 what then was your happiness? for I testify to you, that if possible, your eyes having plucked out, ye would have given to me;
Saboda haka, yanzu ina murnar taku? Domin ina shaidar ku, idan mai yiwuwa ne, da kun kwakulo idanunku, kun ba ni.
16 so that your enemy have I become, being true to you?
To kenan, na zama makiyin ku ne saboda na gaya maku gaskiya?
17 they are zealous for you — [yet] not well, but they wish to shut us out, that for them ye may be zealous;
Suna neman ku da himma ba domin wani alheri ba ne. Suna so su raba ni da ku domin ku bi su.
18 and [it is] good to be zealously regarded, in what is good, at all times, and not only in my being present with you;
Yana da kyau ko yaushe a yi himma domin dalilai masu kyau, ba kuma kawai sa'adda ina tare da ku ba.
19 my little children, of whom again I travail in birth, till Christ may be formed in you,
'Ya'yana kanana, sabili da ku ina cikin zafin nakuda kuma sai Almasihu ya samu kafuwa cikinku.
20 and I was wishing to be present with you now, and to change my voice, because I am in doubt about you.
Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canza muryata, domin ina damuwa a kanku kwarai.
21 Tell me, ye who are willing to be under law, the law do ye not hear?
Ku gaya mani, ku da kuke marmarin ku zo karkashin shari'a, ba ku ji abin da shari'ar ta ce ba?
22 for it hath been written, that Abraham had two sons, one by the maid-servant, and one by the free-woman,
A rubuce yake cewa, Ibrahim yana da 'ya'ya maza biyu, daya dan baiwa ne, dayan kuma dan 'yantaciyar mace ne.
23 but he who [is] of the maid-servant, according to flesh hath been, and he who [is] of the free-woman, through the promise;
Abin lura anan, dan baiwar an haife shi ta hanyar mutuntaka ne, amma dan 'yantaciyar macen, an haife shi ta wurin alkawari ne.
24 which things are allegorized, for these are the two covenants: one, indeed, from mount Sinai, to servitude bringing forth, which is Hagar;
Ana iya bayyana abubuwan nan a hanyar kwatanci kamar haka, wadannan mata na kama da alkawarai ne guda biyu. Dayan alkawarin daga dutsen Sinayi ne. Ta haifi 'ya'ya da ke bayi ne su. Ita ce Hajaratu.
25 for this Hagar is mount Sinai in Arabia, and doth correspond to the Jerusalem that now [is], and is in servitude with her children,
Yanzu fa, Hajaratu ita ce dutsen Sinayi da ke Arebiya. Misali ce na Urushalima na yanzu, domin tana cikin bauta tare da 'ya'yanta.
26 and the Jerusalem above is the free-woman, which is mother of us all,
Amma Urushalima da ke bisa 'yantacciya ce, ita ce mahaifiyarmu.
27 for it hath been written, 'Rejoice, O barren, who art not bearing; break forth and cry, thou who art not travailing, because many [are] the children of the desolate — more than of her having the husband.'
Kamar yadda yake a rubuce, “Ki yi murna, ke bakarariya, ke da ba ki taba haihuwa ba. Ki yi shewa na farinciki, ke da ba ki dandana haihuwan da ba. Domin 'ya'yan bakarariya da yawa suke, fiye da ta mace mai miji.”
28 And we, brethren, as Isaac, are children of promise,
Yanzu fa, 'yan'uwa, kamar yadda Ishaku yake, haka muke, wato 'ya'yan alkawari.
29 but as then he who was born according to the flesh did persecute him according to the spirit, so also now;
A lokacin can, shi wanda aka haife shi ta hanyar mutuntaka ya tsananta wa wanda aka haife shi ta hanyar Ruhu. Haka yake har yanzu.
30 but what saith the Writing? 'Cast forth the maid-servant and her son, for the son of the maid-servant may not be heir with the son of the free-woman;'
Amma menene nassi ya ce? “Ka kori baiwar nan tare da danta. Domin dan baiwar nan ba za ya ci gado tare da dan macen nan da ke 'yantacciya ba.”
31 then, brethren, we are not a maid-servant's children, but the free-woman's.
Saboda haka 'yan'uwa, mu ba 'ya'yan baiwa ba ne, a maimakon haka, mu 'ya'yan macen nan ne da ke 'yantacciya.