< Galatians 1 >
1 Paul, an apostle — not from men, nor through man, but through Jesus Christ, and God the Father, who did raise him out of the dead —
Wannan Bulus manzo ne. Manzancina kuwa, bai zo daga mutane ba ko mutum, amma ta wurin Yesu Almasihu da Allah Uba wanda da ya tashe shi daga matattu.
2 and all the brethren with me, to the assemblies of Galatia:
Ni da dukan 'yan'uwa da nake tare da su a nan, ina rubuto maku ku iklisiyoyi da ke a Galatiya.
3 Grace to you, and peace from God the Father, and our Lord Jesus Christ,
Alheri zuwa gare ku da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangjinmu Yesu Almasihu,
4 who did give himself for our sins, that he might deliver us out of the present evil age, according to the will of God even our Father, (aiōn )
wanda ya ba da kansa domin zunubanmu saboda ya kubutar da mu daga wannan mugun zamani, bisa ga nufin Allah da Ubanmu. (aiōn )
5 to whom [is] the glory to the ages of the ages. Amen. (aiōn )
Daukaka ta tabbata a gare shi har abada abadin. (aiōn )
6 I wonder that ye are so quickly removed from Him who did call you in the grace of Christ to another good news;
Na yi mamaki kwarai yadda kuka juya da sauri zuwa wata bishara daban. Na yi mamakin cewa kuna juyawa daga shi wanda ya kira ku ta wurin alherin Almasihu.
7 that is not another, except there be certain who are troubling you, and wishing to pervert the good news of the Christ;
Ba wata bishara, amma akwai wadansu mutane da suke kawo maku rudani kuma suna so su gurbata bisharar Almasihu.
8 but even if we or a messenger out of heaven may proclaim good news to you different from what we did proclaim to you — anathema let him be!
Amma, ko da mu ne ko mala'ika daga sama ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda muka yi shelar ta, la'ananne ne.
9 as we have said before, and now say again, If any one to you may proclaim good news different from what ye did receive — anathema let him be!
Kamar yadda muka fadi maku a da, yanzu kuma ina sake fada, “Idan wani ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda kuka karba, la'ananne ne.”
10 for now men do I persuade, or God? or do I seek to please men? for if yet men I did please — Christ's servant I should not be.
To yanzu ina neman shaidar mutane ne ko Allah? Ina neman in gamshi mutane ne? Idan har yanzu ina kokarin in gamshi mutane ne, ni ba bawan Almasihu ba ne.
11 And I make known to you, brethren, the good news that were proclaimed by me, that it is not according to man,
Ina son ku sani fa 'yan'uwa, cewa bisharar da nake shelar ta ba daga mutane take ba.
12 for neither did I from man receive it, nor was I taught [it], but through a revelation of Jesus Christ,
Ban karbe ta daga mutum ba, ba ma wanda ya koyar mani A maimakon haka, ta wurin wahayin Yesu Almasihu ne zuwa gare ni.
13 for ye did hear of my behaviour once in Judaism, that exceedingly I was persecuting the assembly of God, and wasting it,
Kun riga kun ji game da rayuwa ta a da cikin Yahudanci, yadda da nake da kwazon tsananta wa iklisiyar Allah fiye da misali kuma ina lalatar da ita.
14 and I was advancing in Judaism above many equals in age in mine own race, being more abundantly zealous of my fathers' deliverances,
Ina gaba-gaba cikin Yahudanci fiye da yawancin tsararrakina. A kwazo kuwa fiye da kima game da al'adun ubannina.
15 and when God was well pleased — having separated me from the womb of my mother, and having called [me] through His grace —
Amma ya gamshi Allah ya zabe ni daga cikin mahaifiyata. Ya kira ni ta wurin alherinsa.
16 to reveal His Son in me, that I might proclaim him good news among the nations, immediately I conferred not with flesh and blood,
Ya bayyana dansa a gareni, saboda in yi shelar sa cikin al'ummai. Nan da nan, ban nemi shawarar nama da jini ba
17 nor did I go up to Jerusalem unto those who were apostles before me, but I went away to Arabia, and again returned to Damascus,
kuma ban tafi Urushalima ba wurin wadanda suka zama manzanni kafin ni. Maimakon haka sai na tafi Arebiya, daga nan sai na dawo Dimashku.
18 then, after three years I went up to Jerusalem to enquire about Peter, and remained with him fifteen days,
Bayan shekara uku na je Urushalima don in san Kefas, na zauna da shi na kwana goma sha biyar.
19 and other of the apostles I did not see, except James, the brother of the Lord.
Amma ban ga ko daya daga cikin manzannin ba sai Yakubu kadai, dan'uwan Ubangiji.
20 And the things that I write to you, lo, before God — I lie not;
Duba, a gaban Allah, ba karya nake yi ba cikin abin da na rubuta maku.
21 then I came to the regions of Syria and of Cilicia,
Daga nan sai na je lardin Suriya da Kilikiya.
22 and was unknown by face to the assemblies of Judea, that [are] in Christ,
Har a lokacin babu wanda ya san ni a fuska a iklisiyoyin Yahudiya da suke cikin Almasihu,
23 and only they were hearing, that 'he who is persecuting us then, doth now proclaim good news — the faith that then he was wasting;'
amma sai labari kawai suke ji, “Wanda a da yake tsananta mana yanzu yana shelar bangaskiyar da a da yake rusarwa.”
24 and they were glorifying God in me.
Suna ta daukaka Allah saboda ni.