< Ezekiel 47 >
1 And he causeth me to turn back unto the opening of the house; and lo, water is coming forth from under the threshold of the house eastward, for the front of the house [is] eastward, and the water is coming down from beneath, from the right side of the house, from the south of the altar.
Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
2 And he causeth me to go out the way of the gate northward, and causeth me to turn round the way without, unto the gate that [is] without, the way that is looking eastward, and lo, water is coming forth from the right side.
Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
3 In the going out of the man eastward, and a line in his hand, then he measureth a thousand by the cubit, and he causeth me to pass over into water — water to the ankles.
Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
4 And he measureth a thousand, and causeth me to pass over into water — water to the knees. And he measureth a thousand, and causeth me to pass over — water to the loins.
Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
5 And he measureth a thousand — a stream that I am not able to pass over; for risen have the waters — waters to swim in — a stream that is not passed over.
Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
6 And he saith unto me, 'Hast thou seen, son of man?' and he leadeth me, and bringeth me back unto the edge of the stream.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
7 In my turning back, then, lo, at the edge of the stream [are] very many trees, on this side and on that side.
Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
8 And he saith unto me, 'These waters are going forth unto the east circuit, and have gone down unto the desert, and have entered the sea; unto the sea they are brought forth, and the waters have been healed.
Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
9 And it hath come to pass, every living creature that teemeth, whithersoever the streams come, doth live: and there hath been great abundance of fish, for these waters have come thither, and they are healed; and every thing whither the stream cometh hath lived.
Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
10 And it hath come to pass, fishers do stand by it, from En-Gedi even unto En-Eglaim; a spreading place of nets they are; according to their own kind is their fish, as the fish of the great sea, very many.
Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
11 Its miry and its marshy places — they are not healed; to salt they have been given up.
Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
12 And by the stream there cometh up on its edge, on this side and on that side, every [kind of] fruit-tree whose leaf fadeth not, and not consumed is its fruit, according to its months it yieldeth first-fruits, because its waters from the sanctuary are coming forth; and its fruits hath been for food, and its leaf for medicine.
’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
13 'Thus said the Lord Jehovah: This [is] the border whereby ye inherit the land, according to the twelve tribes of Israel; Joseph [hath] portions.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
14 And ye have inherited it, one as well as another, in that I have lifted up My hand to give it to your fathers; and this land hath fallen to you in inheritance.
Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
15 'And this [is] the border of the land at the north quarter; from the great sea, the way of Hethlon, at the coming in to Zedad:
“Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
16 Hamath, Berothah, Sibraim, that [is] between the border of Damascus and the border of Hamath; Hazar-Hatticon, that [is] at the coast of Havran.
Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
17 And the border from the sea hath been Hazar-Enan, the border of Damascus, and Zaphon at the north, and the border of Hamath: and [this is] the north quarter.
Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
18 'And the east quarter [is] from between Havran, and Damascus, and Gilead, and the land of Israel, [to] the Jordan; from the border over-against the eastern sea ye measure: and [this is] the east quarter.
A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
19 'And the south quarter southward [is] from Tamar unto the waters of Meriboth-Kadesh, the stream unto the great sea: and [this is] the south quarter southward.
A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
20 'And the west quarter [is] the great sea, from the border till over-against the coming in to Hamath: this [is] the west quarter.
A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
21 'And ye have divided this land to you, according to the tribes of Israel;
“Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
22 and it hath come to pass, ye separate it for an inheritance to yourselves, and to the sojourners who are sojourning in your midst, who have begotten sons in your midst, and they have been to you as native, with the sons of Israel, with you they are separated for an inheritance in the midst of the tribes of Israel.
Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
23 And it hath come to pass, in the tribe with which the sojourner sojourneth, there ye give his inheritance — an affirmation of the Lord Jehovah.
A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.