< Exodus 12 >

1 And Jehovah speaketh unto Moses and unto Aaron, in the land of Egypt, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna a Masar,
2 'This month [is] to you the chief of months — it [is] the first to you of the months of the year;
“Wannan wata za tă zama a gare ku wata na farko, wata na fari na shekararku.
3 speak ye unto all the company of Israel, saying, In the tenth of this month — they take to them each man a lamb for the house of the fathers, a lamb for a house.
Ka faɗa wa dukan jama’ar Isra’ila cewa a rana ta goma ga wannan wata, kowane mutum zai ɗauki ɗan rago domin iyalinsa, ɗaya domin kowane gida.
4 '(And if the household be too few for a lamb, then hath he taken, he and his neighbour who is near unto his house, for the number of persons, each according to his eating ye do count for the lamb, )
In akwai wani gidan da ba za su iya cinye rago guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki rago guda gwargwadon yawansu, bisa ga abin da mutum guda zai ci.
5 a lamb, a perfect one, a male, a son of a year, let be to you; from the sheep or from the goats ye do take [it].
Dabbobin da za ku zaɓa, dole su zama bana ɗaya, namiji marar tabo, za ku kuma kamo su daga cikin tumaki ko awaki.
6 'And it hath become a charge to you, until the fourteenth day of this month, and the whole assembly of the company of Israel have slaughtered it between the evenings;
Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.
7 and they have taken of the blood, and have put on the two side-posts, and on the lintel over the houses in which they eat it.
Sa’an nan za su ɗauki jinin, su shafa a gefen da yake saman dogaran ƙofa na gidajen da suke cin naman dabbobin.
8 'And they have eaten the flesh in this night, roast with fire; with unleavened things and bitters they do eat it;
A wannan dare, za su gasa naman, su ci da ganyaye masu ɗaci, da kuma burodi marar yisti.
9 ye do not eat of it raw, or boiled at all in water, but roast with fire, its head with its legs, and with its inwards;
Kada ku ci nama ɗanye, ko kuma dafaffe, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kuma kayan cikin.
10 and ye do not leave of it till morning, and that which is remaining of it till morning with fire ye do burn.
Kada ku bar kome yă kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi.
11 'And thus ye do eat it: your loins girded, your sandals on your feet, and your staff in your hand, and ye have eaten it in haste; it is Jehovah's passover,
Ga yadda za ku ci shi, ku yi ɗamara, takalma kuwa a ƙafafunku, kuna riƙe da sandunan tafiya a hannunku. Ku ci shi da gaggawa; Bikin Ƙetarewa ne na Ubangiji.
12 and I have passed over through the land of Egypt during this night, and have smitten every first-born in the land of Egypt, from man even unto beast, and on all the gods of Egypt I do judgments; I [am] Jehovah.
“A wannan dare, zan ratsa Masar, in bugi kowane ɗan fari, na mutum da na dabba, zan kuma hukunta dukan gumakan Masar. Ni ne Ubangiji.
13 'And the blood hath become a sign for you on the houses where ye [are], and I have seen the blood, and have passed over you, and a plague is not on you for destruction in My smiting in the land of Egypt.
Jinin zai zama alama a gare ku, a gidajen da kuke; sa’ad da kuwa na ga jinin, zan ƙetare ku. Ba wata annoba mai hallakarwa da za tă taɓa ku yayinda na bugi Masar.
14 'And this day hath become to you a memorial, and ye have kept it a feast to Jehovah to your generations; — a statute age-during; ye keep it a feast.
“Wannan rana za tă zama muku abin tunawa dukan zamananku masu zuwa, za ku kiyaye ta kamar biki ga Ubangiji, dawwammamiyar farilla ce har abada.
15 Seven days ye eat unleavened things; only — in the first day ye cause leaven to cease out of your houses; for any one eating anything fermented from the first day till the seventh day, even that person hath been cut off from Israel.
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti. A rana ta fari, za ku fid da yisti daga gidajenku gama duk wanda ya ci abu mai yisti daga rana ta fari har zuwa rana ta bakwai, za a fid da shi daga Isra’ila.
16 'And in the first day [is] a holy convocation, and in the seventh day ye have a holy convocation; any work is not done in them, only that which is eaten by any person — it alone is done by you,
A rana ta fari, za ku yi taro mai tsarki, haka kuma za ku sāke yi a rana ta bakwai. Kada ku yi aiki a waɗannan ranaku, sai dai ku shirya abinci domin kowa, abin da za ku yi ke nan kawai.
17 and ye have observed the unleavened things, for in this self-same day I have brought out your hosts from the land of Egypt, and ye have observed this day to your generations — a statute age-during.
“Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti domin a wannan rana ce na fitar da ku ɓangare-ɓangare daga Masar. Ku kiyaye wannan rana ta zama muku dawwammamiyar farilla wa tsara masu zuwa.
18 'In the first [month], in the fourteenth day of the month, in the evening, ye do eat unleavened things until the one and twentieth day of the month, at evening;
A wata na fari, za ku ci burodi marar yisti daga yammancin ranar goma sha huɗu har zuwa yammancin ranar ashirin da ɗaya.
19 seven days leaven is not found in your houses, for any [one] eating anything fermented — that person hath been cut off from the company of Israel, among the sojourners or among the natives of the land;
Kada a sami yisti a gidajenku har kwana bakwai. Kuma duk wanda ya ci wani abu mai yisti, za a fid da shi daga taron jama’ar Isra’ila, ko baƙo ne, ko haifaffen ɗan ƙasa.
20 anything fermented ye do not eat, in all your dwellings ye do eat unleavened things.'
Kada ku ci wani abincin da aka yi da yisti. Ko’ina kuka zauna, dole ku ci burodi marar yisti.”
21 And Moses calleth for all the elders of Israel, and saith unto them, 'Draw out and take for yourselves [from] the flock, for your families, and slaughter the passover-sacrifice;
Sa’an nan Musa ya kira dukan dattawan Isra’ila ya ce musu, “Ku je da sauri ku zaɓi dabbobin iyalanku, ku yanka ragon Bikin Ƙetarewa.
22 and ye have taken a bunch of hyssop, and have dipped [it] in the blood which [is] in the basin, and have struck [it] on the lintel, and on the two side-posts, from the blood which [is] in the basin, and ye, ye go not out each from the opening of his house till morning.
Ku ɗauki ƙunshin itacen hizzob, ku tsoma cikin jinin da yake a kwano, ku yayyafa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada wani daga cikinku yă fita daga ƙofar gidansa sai da safe.
23 'And Jehovah hath passed on to smite the Egyptians, and hath seen the blood on the lintel, and on the two side-posts, and Jehovah hath passed over the opening, and doth not permit the destruction to come into your houses to smite.
Sa’ad da Ubangiji yake ratsa ƙasar don yă bugi Masarawa, zai ga jinin a bisa da kuma gefen madogaran ƙofa, zai ƙetare ƙofar, ba zai bar mai hallakawa yă shiga gidajenku, yă buge ku ba.
24 'And ye have observed this thing, for a statute to thee, and to thy sons — unto the age;
“Ku kiyaye waɗannan dokokin a matsayin dawwammamiyar farilla, da ku da’ya’yanku har abada.
25 and it hath been, when ye come in unto the land which Jehovah giveth to you, as He hath spoken, that ye have kept this service;
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku yadda ya alkawarta, ku kiyaye wannan biki.
26 and it hath come to pass when your sons say unto you, What [is] this service ye have?
Sa’ad da kuma’ya’yanku suka tambaye ku, ‘Mece ce manufar wannan biki?’
27 that ye have said, A sacrifice of passover it [is] to Jehovah, who passed over the houses of the sons of Israel in Egypt, in His smiting the Egyptians, and our houses He delivered.'
Sai ku faɗa musu, ‘Hadaya ce ta Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra’ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’” Sai mutane suka rusuna, suka yi sujada.
28 And the people bow and do obeisance, and the sons of Israel go and do as Jehovah commanded Moses and Aaron; so have they done.
Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
29 And it cometh to pass, at midnight, that Jehovah hath smitten every first-born in the land of Egypt, from the first-born of Pharaoh who is sitting on his throne, unto the first-born of the captive who [is] in the prison-house, and every first-born of beasts.
Da tsakar dare, sai Ubangiji ya karkashe dukan’ya’yan fari a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir’auna, wato, magājinsa, har zuwa ɗan fari na ɗan sarƙa da yake kurkuku, har da’ya’yan fari na dabbobi.
30 And Pharaoh riseth by night, he and all his servants, and all the Egyptians, and there is a great cry in Egypt, for there is not a house where there is not [one] dead,
Fir’auna da dukan fadawansa da kuma dukan Masarawa, suka tashi a cikin daren da kuka mai zafi, aka kuma ji kukan a ko’ina a cikin ƙasar Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba.
31 and he calleth for Moses and for Aaron by night, and saith, 'Rise, go out from the midst of my people, both ye and the sons of Israel, and go, serve Jehovah according to your word;
A cikin daren, Fir’auna ya aika a kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tashi, ku da jama’arku, ku fita daga cikin jama’ata. Ku tafi, ku bauta wa Ubangiji yadda kuka ce.
32 both your flock and your herd take ye, as ye have spoken, and go; then ye have blessed also me.'
Ku kwashi garkunanku na tumaki da na awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.”
33 And the Egyptians are urgent on the people, hasting to send them away out of the land, for they said, 'We are all dead;'
Masarawa suka matsa wa Isra’ilawa su fita daga ƙasarsu da sauri. Gama mutanen Masar sun ce, “Ai, za mu mutu duka, in ba su tafi ba!”
34 and the people taketh up its dough before it is fermented, their kneading-troughs [are] bound up in their garments on their shoulder.
Sai mutanen suka ɗauki garin da sun kwaɓa ba yisti a ciki, tare da ƙwaryansu na aikin kwaɓan, suka nannaɗe su a mayafansu, suka rataye a kafaɗunsu.
35 And the sons of Israel have done according to the word of Moses, and they ask from the Egyptians vessels of silver and vessels of gold, and garments;
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya umarce su, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi.
36 and Jehovah hath given the grace of the people in the eyes of the Egyptians, and they cause them to ask, and they spoil the Egyptians.
Ubangiji kuwa ya sa Isra’ilawa suka yi farin jini a wurin Masarawa, Masarawa kuma suka saki hannu wa mutanen, suka ba su duk abin da suka roƙa; ta haka Isra’ilawa suka washe Masarawa.
37 And the sons of Israel journey from Rameses to Succoth, about six hundred thousand men on foot, apart from infants;
Isra’ilawa suka kama tafiya daga Rameses zuwa Sukkot. Akwai maza dubu ɗari shida da suke tafiya da ƙafa, ban da mata da yara.
38 and a great rabble also hath gone up with them, and flock and herd — very much cattle.
Waɗansu mutane da yawa da ba Isra’ilawa ba, suka haura tare da su, da garkunan shanu, da na tumaki da awaki.
39 And they bake with the dough which they have brought out from Egypt unleavened cakes, for it hath not fermented; for they have been cast out of Egypt, and have not been able to delay, and also provision they have not made for themselves.
Suka toya burodi marar yisti da garin da aka kwaɓa wanda suka kawo daga Masar. Garin da aka kwaɓan ba shi da yisti, domin an kore su daga Masar, ba su kuwa sami damar shirya wa kansu abinci ba.
40 And the dwelling of the sons of Israel which they have dwelt in Egypt [is] four hundred and thirty years;
Zaman da Isra’ilawa suka yi a Masar, ya kai shekara 430.
41 and it cometh to pass, at the end of four hundred and thirty years — yea, it cometh to pass in this self-same day — all the hosts of Jehovah have gone out from the land of Egypt.
A ranar da shekara 430 ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan ɓangare-ɓangare na mutanen Ubangiji suka bar Masar.
42 A night of watchings it [is] to Jehovah, to bring them out from the land of Egypt; it [is] this night to Jehovah of watchings to all the sons of Israel to their generations.
Gama Ubangiji ya yi tsaro a wannan dare, domin yă fitar da su daga Masar, a wannan dare, dole dukan Isra’ilawa su yi tsaro, don su girmama Ubangiji, cikin dukan tsararraki masu zuwa.
43 And Jehovah saith unto Moses and Aaron, 'This [is] a statute of the passover; Any son of a stranger doth not eat of it;
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Waɗannan ne ƙa’idodin Bikin Ƙetarewa. “Ba baƙon da zai ci shi.
44 and any man's servant, the purchase of money, when thou hast circumcised him — then he doth eat of it;
Duk bawan da kuka sayo, yana iya ci, in dai an yi masa kaciya,
45 a settler or hired servant doth not eat of it;
amma wanda ba ya zama tare da ku na ɗinɗinɗin, da kuma wanda aka ɗauki hayansa, ba zai ci ba.
46 in one house it is eaten, thou dost not carry out of the house [any] of the flesh without, and a bone ye do not break of it;
“Dole a ci shi a cikin gida ɗaya; kada a kai naman waje. Kada a karya wani daga ƙasusuwansa.
47 all the company of Israel do keep it.
Dole dukan taron jama’ar Isra’ila su yi bikin.
48 'And when a sojourner sojourneth with thee, and hath made a passover to Jehovah, every male of his [is] to be circumcised, and then he doth come near to keep it, and he hath been as a native of the land, but any uncircumcised one doth not eat of it;
“Baƙon da yake zama tare da ku da yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi wa dukan mazan da suke cikin gidansa kaciya; sa’an nan ne zai iya yin abubuwa kamar haifaffen ɗan ƙasa.
49 one law is to a native, and to a sojourner who is sojourning in your midst.'
Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
50 And all the sons of Israel do as Jehovah commanded Moses and Aaron; so have they done.
Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
51 And it cometh to pass in this self-same day, Jehovah hath brought out the sons of Israel from the land of Egypt, by their hosts.
A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.

< Exodus 12 >