< Deuteronomy 24 >
1 'When a man doth take a wife, and hath married her, and it hath been, if she doth not find grace in his eyes (for he hath found in her nakedness of anything), and he hath written for her a writing of divorce, and given [it] into her hand, and sent her out of his house,
Idan mutum ya auri mata, daga baya ba tă gamshe shi ba domin ya gano wani abu marar kyau game da ita, ya ba ta takardar saki, ya kuma kore ta daga gidansa,
2 and she hath gone out of his house, and hath gone and been another man's,
in bayan ta bar gidansa ta zama matar wani dabam,
3 and the latter man hath hated her, and written for her a writing of divorce, and given [it] into her hand, and sent her out of his house, or when the latter man dieth, who hath taken her to himself for a wife:
sai mijinta na biyu ya ƙi ta, ya ba ta takardan saki, ya kore ta daga gidansa, ko kuwa ya mutu,
4 'Her former husband who sent her away is not able to turn back to take her to be to him for a wife, after that she hath become defiled; for an abomination it [is] before Jehovah, and thou dost not cause the land to sin which Jehovah thy God is giving to thee — an inheritance.
to, kada mijinta na farko, wanda ya sake ta yă sāke aurenta, tun da yake ta ƙazantu. Wannan zai zama abin ƙyama a gaban Ubangiji. Kada ku kawo zunubi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo.
5 'When a man taketh a new wife, he doth not go out into the host, and [one] doth not pass over unto him for anything; free he is at his own house one year, and hath rejoiced his wife whom he hath taken.
In mutum bai daɗe da aure ba, kada a sa yă je yaƙi, ko yă yi wani aiki. Gama zai huta shekara guda a gida, yă faranta wa matar da ya aura rai.
6 'None doth take in pledge millstones, and rider, for life it [is] he is taking in pledge.
Kada ku karɓi jinginar dutsen niƙa tare da ɗan dutsen niƙan, domin yin haka zai zama karɓar jinginar rai ne.
7 'When a man is found stealing a person, of his brethren, of the sons of Israel, and hath tyrannized over him, and sold him, then hath that thief died, and thou hast put away the evil thing out of thy midst.
Idan aka kama wani yana satar ɗan’uwansa mutumin Isra’ila domin yă sa ya zama bawansa, ko yă sayar da shi, sai a kashe ɓarawon nan. Haka za ku kawar da mugunta daga cikinku.
8 'Take heed, in the plague of leprosy, to watch greatly, and to do according to all that the priests, the Levites, teach you; as I have commanded them ye observe to do;
Game da cututtukan kuturta, sai ku lura, ku yi yadda firistocin da suke Lawiyawa suka umarce ku. Dole ku lura ku bi abin da na umarce su.
9 remember that which Jehovah thy God hath done to Miriam in the way, in your coming out of Egypt.
Ku tuna da abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Miriyam a hanya, bayan kun fito Masar.
10 'When thou liftest up on thy brother a debt of anything, thou dost not go in unto his house to obtain his pledge;
Sa’ad da kuka ba da rance na kowane iri ga maƙwabcinku, kada ku shiga gidansa don karɓar wani abu a matsayin jingina.
11 at the outside thou dost stand, and the man on whom thou art lifting [it] up is bringing out unto thee the pledge at the outside.
Ku tsaya a waje ku bar mutumin da yake karɓan rancen yă kawo muku abin da zai bayar a matsayin jingina.
12 'And if he is a poor man, thou dost not lie down with his pledge;
In matalauci ne, kada ku kwana da abin da zai bayar a matsayin jingina a wurinku.
13 thou dost certainly give back to him the pledge at the going in of the sun, and he hath lain down in his own raiment, and hath blessed thee; and to thee it is righteousness before Jehovah thy God.
Ku mayar da rigarsa a fāɗuwar rana saboda yă sami abin rufuwa. Yin haka zai sa yă gode muku, za a kuma ɗauka wannan a matsayin aikin adalci da kuka yi a gaban Ubangiji Allahnku.
14 'Thou dost not oppress a hireling, poor and needy, of thy brethren or of thy sojourner who is in thy land within thy gates;
Kada ku zalunci ɗan ƙodago matalauci da mabukaci, ko da shi ɗan’uwanku ne mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a cikin garuruwanku.
15 in his day thou dost give his hire, and the sun doth not go in upon it, for he [is] poor, and unto it he is lifting up his soul, and he doth not cry against thee unto Jehovah, and it hath been in thee — sin.
Ku biya kuɗin aikinsa kowace rana kafin fāɗuwar rana, domin shi matalauci ne, yana kuma sa rai a kan wannan hakkin ne, don kada ya yi wa Ubangiji kuka a kanku, har yă zama laifi a gare ku.
16 'Fathers are not put to death for sons, and sons are not put to death for fathers — each for his own sin, they are put to death.
Ba za a kashe iyaye a maimakon’ya’yansu ba, ba kuwa za a kashe’ya’ya a maimakon iyayensu ba; kowa ya yi zunubi, shi za a kashe.
17 'Thou dost not turn aside the judgment of a fatherless sojourner, nor take in pledge the garment of a widow;
Ba za ku danne hakkin baƙon da yake zama a cikinku ko na marayu ba, ba za ku ɗauki rigar matar da mijinta ya mutu a matsayin jingina ba.
18 and thou hast remembered that a servant thou hast been in Egypt, and Jehovah thy God doth ransom thee from thence; therefore I am commanding thee to do this thing.
Ku tuna dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku kuwa ya fisshe daga can. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.
19 'When thou reapest thy harvest in thy field, and hast forgotten a sheaf in a field, thou dost not turn back to take it; to the sojourner, to the fatherless, and to the widow, it is; so that Jehovah thy God doth bless thee in all the work of thy hands.
Sa’ad da kuke girbi a gonarku, sai kuka manta da dami, kada ku koma don ku ɗauka. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa, saboda Ubangiji Allahnku yă albarkace ku a cikin dukan aikin hannuwanku.
20 'When thou beatest thine olive, thou dost not examine the branch behind thee; to the sojourner, to the fatherless, and to the widow, it is.
Sa’ad da kuka kakkaɓe’ya’yan zaitun daga itatuwanku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
21 'When thou cuttest thy vineyard, thou dost not glean behind thee; to the sojourner, to the fatherless, and to the widow, it is;
Sa’ad da kuka yi girbin inabi a gonar inabinku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
22 and thou hast remembered that a servant thou hast been in the land of Egypt; therefore I am commanding thee to do this thing.
Ku tuna dā ku bayi ne Masar. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.