< Daniel 11 >
1 'And I, in the first year of Darius the Mede, my standing [is] for a strengthener, and for a stronghold to him;
A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
2 and, now, truth I declare to thee, Lo, yet three kings are standing for Persia, and the fourth doth become far richer than all, and according to his strength by his riches he stirreth up the whole, with the kingdom of Javan.
“Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
3 And a mighty king hath stood, and he hath ruled a great dominion, and hath done according to his will;
Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
4 and according to his standing is his kingdom broken, and divided to the four winds of the heavens, and not to his posterity, nor according to his dominion that he ruled, for his kingdom is plucked up — and for others apart from these.
Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
5 'And a king of the south — even of his princes — doth become strong, and doth prevail against him, and hath ruled; a great dominion [is] his dominion.
“Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
6 'And at the end of years they do join themselves together, and a daughter of the king of the south doth come in unto the king of the north to do upright things; and she doth not retain the power of the arm; and he doth not stand, nor his arm; and she is given up, she, and those bringing her in, and her child, and he who is strengthening her in [these] times.
Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
7 'And [one] hath stood up from a branch of her roots, [in] his station, and he cometh in unto the bulwark, yea, he cometh into a stronghold of the king of the south, and hath wrought against them, and hath done mightily;
“Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
8 and also their gods, with their princes, with their desirable vessels of silver and gold, into captivity he bringeth [into] Egypt; and he doth stand more years than the king of the north.
Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
9 'And the king of the south hath come into the kingdom, and turned back unto his own land;
Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
10 and his sons stir themselves up, and have gathered a multitude of great forces, and he hath certainly come in, and overflowed, and passed through, and he turneth back, and they stir themselves up unto his stronghold.
’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
11 And the king of the south doth become embittered, and hath gone forth and fought with him, with the king of the north, and hath caused a great multitude to stand, and the multitude hath been given into his hand,
“Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
12 and he hath carried away the multitude, his heart is high, and he hath caused myriads to fall, and he doth not become strong.
Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
13 'And the king of the north hath turned back, and hath caused a multitude to stand, greater than the first, and at the end of the times a second time he doth certainly come in with a great force, and with much substance;
Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
14 and in those times many do stand up against the king of the south, and sons of the destroyers of thy people do lift themselves up to establish the vision — and they have stumbled.
“A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
15 'And the king of the north cometh in, and poureth out a mount, and hath captured fenced cities; and the arms of the south do not stand, nor the people of his choice, yea, there is no power to stand.
Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
16 And he who is coming unto him doth according to his will, and there is none standing before him; and he standeth in the desirable land, and [it is] wholly in his hand.
Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
17 And he setteth his face to go in with the strength of his whole kingdom, and upright ones with him; and he hath wrought, and the daughter of women he giveth to him, to corrupt her; and she doth not stand, nor is for him.
Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
18 'And he turneth back his face to the isles, and hath captured many; and a prince hath caused his reproach of himself to cease; without his reproach he turneth [it] back to him.
Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
19 And he turneth back his face to the strongholds of his land, and hath stumbled and fallen, and is not found.
Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
20 'And stood up on his station hath [one] causing an exactor to pass over the honour of the kingdom, and in a few days he is destroyed, and not in anger, nor in battle.
“Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
21 'And stood up on his station hath a despicable one, and they have not given unto him the honour of the kingdom, and he hath come in quietly, and hath strengthened the kingdom by flatteries.
“Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
22 And the arms of the flood are overflowed from before him, and are broken; and also the leader of the covenant.
Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
23 And after they join themselves unto him, he worketh deceit, and hath increased, and hath been strong by a few of the nation.
Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
24 Peaceably even into the fertile places of the province He cometh, and he hath done that which his fathers did not, nor his fathers' fathers; prey, and spoil, and substance, to them he scattereth, and against fenced places he deviseth his devices, even for a time.
Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
25 'And he stirreth up his power and his heart against the king of the south with a great force, and the king of the south stirreth himself up to battle with a very great and mighty force, and standeth not, for they devise devices against him,
“Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
26 and those eating his portion of food destroy him, and his force overfloweth, and fallen have many wounded.
Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
27 'And both of the kings' hearts [are] to do evil, and at one table they speak lies, and it doth not prosper, for yet the end [is] at a time appointed.
Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
28 And he turneth back [to] his land with great substance, and his heart [is] against the holy covenant, and he hath wrought, and turned back to his land.
“Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
29 At the appointed time he turneth back, and hath come against the south, and it is not as the former, and as the latter.
“A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
30 And ships of Chittim have come in against him, and he hath been pained, and hath turned back, and hath been insolent toward the holy covenant, and hath wrought, and turned back, and he understandeth concerning those forsaking the holy covenant.
Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
31 And strong ones out of him stand up, and have polluted the sanctuary, the stronghold, and have turned aside the continual [sacrifice], and appointed the desolating abomination.
“Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
32 And those acting wickedly [against] the covenant, he defileth by flatteries; and the people knowing their God are strong, and have wrought.
Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
33 And the teachers of the people give understanding to many; and they have stumbled by sword, and by flame, by captivity, and by spoil — days.
“Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
34 And in their stumbling, they are helped — a little help, and joined to them have been many with flatteries.
Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
35 And some of the teachers do stumble for refining by them, and for purifying, and for making white — till the end of the time, for [it is] yet for a time appointed.
Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
36 'And the king hath done according to his will, and exalteth himself, and magnifieth himself against every god, and against the God of gods he speaketh wonderful things, and hath prospered till the indignation hath been completed, for that which is determined hath been done.
“Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
37 And unto the God of his fathers he doth not attend, nor to the desire of women, yea, to any god he doth not attend, for against all he magnifieth himself.
Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
38 And to the god of strongholds, on his station, he giveth honour; yea, to a god whom his fathers knew not he giveth honour, with gold, and with silver, and with precious stone, and with desirable things.
A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
39 And he hath dealt in the fortresses of the strongholds with a strange god whom he hath acknowledged; he multiplieth honour, and hath caused them to rule over many, and the ground he apportioneth at a price.
Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
40 'And at the time of the end, push himself forward with him doth a king of the south, and storm against him doth a king of the north, with chariot, and with horsemen, and with many ships; and he hath come in to the lands, and hath overflowed, and passed over,
“A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
41 and hath come into the desirable land, and many do stumble, and these escape from his hand: Edom, and Moab, and the chief of the sons of Ammon.
Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
42 'And he sendeth forth his hand upon the lands, and the land of Egypt is not for an escape;
Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
43 and he hath ruled over treasures of gold and of silver, and over all the desirable things of Egypt, and Lubim and Cushim [are] at his steps.
Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
44 'And reports trouble him out of the east and out of the north, and he hath gone forth in great fury to destroy, and to devote many to destruction;
Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
45 and he planteth the tents of his palace between the seas and the holy desirable mountain, and hath come unto his end, and there is no helper to him.
Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.