< 2 Samuel 14 >
1 And Joab son of Zeruial knoweth that the heart of the king [is] on Absalom,
Yowab, ɗan Zeruhiya ya gane cewa zuriyar sarki ta koma ga Absalom.
2 and Joab sendeth to Tekoah, and taketh thence a wise woman, and saith unto her, 'Feign thyself a mourner, I pray thee, and put on, I pray thee, garments of mourning, and anoint not thyself with oil, and thou hast been as a woman these many days mourning for the dead,
Saboda haka Yowab ya aiki wani zuwa Tekowa, ya sa a zo da wata mace mai hikima. Ya ce mata, “Ki yi kamar kina makoki. Ki sa rigar makoki, kada kuwa ki shafa mai. Ki yi kamar macen da ta yi kwanaki da yawa, tana makokin matattu.
3 and thou hast gone unto the king, and spoken unto him, according to this word;' and Joab putteth the words into her mouth.
Sa’an nan ki je wurin sarki, ki ce masa haka.” Sai Yowab ya faɗa mata duk abin da za tă faɗa.
4 And the woman of Tekoah speaketh unto the king, and falleth on her face to the earth, and doth obeisance, and saith, 'Save, O king.'
Da macen da ta fito daga Tekowa ta je wajen sarki, sai ta rusuna har ƙasa don bangirma, sai ta ce, “Ka taimake ni, ya sarki!”
5 And the king saith to her, 'What — to thee?' and she saith, 'Truly a widow woman [am] I, and my husband dieth,
Sarki ya ce mata, “Mece ce matsalarki?” Sai ta ce, “Tabbatacce, ni gwauruwa ce; mijina ya mutu.
6 and thy maid-servant hath two sons; and they strive both of them in a field, and there is no deliverer between them, and the one smiteth the other, and putteth him to death;
Baiwarka tana da’ya’ya maza biyu. Suka yi faɗa da juna a fili, kuma ba wanda yake can don yă raba su. Ɗayan ya bugi ɗayan, ya kashe shi.
7 and lo, the whole family hath risen against thy maid-servant, and say, Give up him who smiteth his brother, and we put him to death for the life of his brother whom he hath slain, and we destroy also the heir; and they have quenched my coal which is left — so as not to set to my husband a name and remnant on the face of the ground.'
To, ga duk iyali sun hau kan baiwarka, suna cewa, ‘Ki ba mu ɗayan da ya kashe ɗan’uwansa mu kashe don ran ɗan’uwansa da ya kashe; sa’an nan za mu hallaka magājin shi ma.’ Za su kashe garwashin wuta mai ci da nake da shi kaɗai, su bar mijina ba suna, ba jika, a duniya.”
8 And the king saith unto the woman, 'Go to thine house, and I give charge concerning thee.'
Sarki ya ce wa macen, “Koma gida, zan ba da umarni a madadinki.”
9 And the woman of Tekoah saith unto the king, 'On me, my lord, O king, [is] the iniquity, and on the house of my father; and the king and his throne [are] innocent.'
Amma macen da ta fito daga Tekowa ta ce, “Ranka yă daɗe, sarki! Bari alhakin shari’arka yă kasance a kaina da gidan mahaifina, kai sarki da gidan mulkinka, ba ku da laifi a ciki.”
10 And the king saith, 'He who speaketh [aught] unto thee, and thou hast brought him unto me, then he doth not add any more to come against thee.'
Sai sarki ya ce, “In wani ya yi miki magana, ki kawo shi wurina, ba zai kuwa ƙara damunki ba.”
11 And she saith, 'Let, I pray thee, the king remember by Jehovah thy God, that the redeemer of blood add not to destroy, and they destroy not my son;' and he saith, 'Jehovah liveth; if there doth fall of the hair of thy son to the earth.'
Sai ta ce, “To, bari sarki yă rantse da Ubangiji Allahnsa don yă hana mai ramako yin ƙarin hallakawar da aka yi, domin kada a hallaka ɗana.” Sai ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, babu gashi guda na ɗanki da zai fāɗi ƙasa.”
12 And the woman saith, 'Let, I pray thee, thy maid-servant speak unto my lord the king a word;' and he saith, 'Speak.'
Sai matar ta ce, “Bari baiwarka ta ƙara yin magana sau ɗayan nan wa ranka yă daɗe.” Ya ce, “Ki faɗa.”
13 And the woman saith, 'And why hast thou thought thus concerning the people of God? yea, the king is speaking this thing as a guilty one, in that the king hath not brought back his outcast;
Matar ta ce, “To, don me ka yi wa mutanen Allah irin wannan abu? Sa’ad da sarki ya ce haka, ashe, ba ka hukunta kanka ke nan ba, tun da yake sarki bai yarda ɗansa yă komo gida ba?
14 for we do surely die, and [are] as water which is running down to the earth, which is not gathered, and God doth not accept a person, and hath devised devices in that the outcast is not outcast by Him.
Kamar ruwan da ya zuba a ƙasa, wanda ba a iya kwasa, haka dole mu mutu. Amma Allah ba ya ɗaukan rai; a maimako, yakan ƙirƙiro hanyoyi domin mutumin da aka kora kada yă kasance yasasshe daga gare shi.
15 'And now that I have come to speak unto the king my lord this word, [it is] because the people made me afraid, and thy maid-servant saith, Let me speak, I pray thee, unto the king; it may be the king doth do the word of his handmaid,
“Yanzu ga shi na zo don in faɗa wannan wa ranka yă daɗe sarki, don mutane sun tsorata ni. Baiwarka ta yi tunani ta ce, ‘Zan yi magana wa sarki; wataƙila yă yi abin da baiwarsa ta roƙa.
16 for the king doth hearken to deliver his handmaid out of the paw of the man [seeking] to destroy me and my son together out of the inheritance of God,
Wataƙila sarki zai yarda yă ceci baiwarsa daga hannun mutumin nan da yake ƙoƙari yă hallaka ni da ɗana daga gādon da Allah ya ba mu.’
17 and thy maid-servant saith, Let, I pray thee, the word of my lord the king be for ease; for as a messenger of God so [is] my lord the king, to understand the good and the evil; and Jehovah thy God is with thee.'
“Yanzu kuwa baiwarka tana cewa, ‘Bari magana ranka yă daɗe sarki yă ba ni hutu, gama ranka yă daɗe sarki yana kama da mala’ikan Allah cikin rarrabe nagarta da mugunta. Bari Ubangiji Allahnka yă kasance tare da kai.’”
18 And the king answereth and saith unto the woman, 'Do not, I pray thee, hide from me the thing that I am asking thee;' and the woman saith, 'Let, I pray thee, my lord the king speak.'
Sai sarki ya ce wa matar, “Kada ki ɓoye mini kome daga abin da zan tambaye ki.” Matar ta ce, “Bari ranka yă daɗe sarki yă yi tambaya.”
19 And the king saith, 'Is the hand of Joab with thee in all this?' And the woman answereth and saith, 'Thy soul liveth, my lord, O king, none [doth turn] to the right or to the left from all that my lord the king hath spoken; for thy servant Joab he commanded me, and he put in the mouth of thy maid-servant all these words;
Sarki ya ce, “Anya, babu hannun Yowab a cikin dukan wannan?” Matar ta ce, “Muddin kana a raye, ranka yă daɗe sarki, ba wanda zai juya dama ko hagu daga wani abin da ranka yă daɗe sarki ya faɗa. I, bawanka Yowab ne ya umarce ni in yi wannan, shi ne kuma ya sa kalmomin nan a bakin baiwarka.
20 in order to bring round the appearance of the thing hath thy servant Joab done this thing, and my lord [is] wise, according to the wisdom of a messenger of God, to know all that [is] in the land.'
Bawanka Yowab ne ya yi haka don yă daidaita al’amura. Ranka yă daɗe yana da hikima iri ta mala’ikan Allah, ya san dukan kome da yake faruwa a ƙasar.”
21 And the king saith unto Joab, 'Lo, I pray thee, thou hast done this thing; and go, bring back the young man Absalom.'
Sarki ya ce wa Yowab, “To, da kyau, zan yi haka. Je ka, ka dawo da saurayin nan Absalom.”
22 And Joab falleth on his face to the earth, and doth obeisance, and blesseth the king, and Joab saith, 'To-day hath thy servant known that I have found grace in thine eyes, my lord, O king, in that the king hath done the word of his servant.'
Yowab ya rusuna har ƙasa don bangirma, ya kuma yi wa sarki kyakkyawar fata. Yowab ya ce, “Yau, bawanka ya sani ya sami tagomashi a gare ka, ranka yă daɗe sarki, gama sarki ya ji roƙon bawansa.”
23 And Joab riseth and goeth to Geshur, and bringeth in Absalom to Jerusalem,
Sa’an nan Yowab ya tafi Geshur ya dawo da Absalom Urushalima.
24 and the king saith, 'Let him turn round unto his house, and my face he doth not see.' And Absalom turneth round unto his house, and the face of the king he hath not seen.
Amma sarki ya ce, “Yă tafi gidansa; kada yă zo yă gan ni.” Saboda haka Absalom ya tafi gidansa, bai kuwa je ganin sarki ba.
25 And like Absalom there was no man [so] fair in all Israel, to praise greatly; from the sole of his foot even unto his crown there was no blemish in him;
A cikin dukan Isra’ila babu wanda ake yabon kyansa kamar Absalom. Tun daga kansa har zuwa tafin ƙafansa babu tabo a jikinsa.
26 and in his polling his head — and it hath been at the end of year by year that he polleth [it], for it [is] heavy on him, and he hath polled it — he hath even weighed out the hair of his head — two hundred shekels by the king's weight.
A duk sa’ad da ya aske gashin kansa (yakan aske kansa lokaci-lokaci sa’ad da ya yi masa nauyi) yakan auna shi, nauyin gashin kuwa yakan kai wajen shekel ɗari biyu a ma’aunin da ake awo.
27 And there are born to Absalom three sons, and one daughter, and her name [is] Tamar; she was a woman of a fair appearance.
Aka haifa wa Absalom’ya’ya uku maza da’ya mace guda. Sunanta Tamar, ta kuwa zama kyakkyawan mace ƙwarai.
28 And Absalom dwelleth in Jerusalem two years of days, and the face of the king he hath not seen;
Absalom ya zauna a Urushalima shekara biyu amma ba tare da ganin fuskar sarki ba.
29 and Absalom sendeth unto Joab, to send him unto the king, and he hath not been willing to come unto him; and he sendeth again a second time, and he hath not been willing to come.
Sai Absalom ya aika a kira masa Yowab don yă aike shi wurin sarki, amma Yowab ya ƙi zuwa. Saboda haka ya sāke aika sau na biyu, amma ya ƙi yă zo.
30 And he saith unto his servants, 'See, the portion of Joab [is] by the side of mine, and he hath barley there; go, and burn it with fire;' and the servants of Absalom burn the portion with fire.
Sai ya ce wa bayinsa, “Duba, gonar Yowab tana gab da tawa, kuma yana da sha’ir a can. Ku je ku sa mata wuta.” Sai bayin Absalom suka sa wa gonar wuta.
31 And Joab riseth and cometh unto Absalom in the house, and saith unto him, 'Why have thy servants burned the portion that I have with fire?'
Sa’an nan Yowab ya tafi gidan Absalom ya ce masa, “Me ya sa bayinka suka sa wa gonata wuta?”
32 And Absalom saith unto Joab, 'Lo, I sent unto thee, saying, Come hither, and I send thee unto the king to say, Why have I come in from Geshur? — good for me while I [am] there — and now, let me see the king's face, and if there is in me iniquity then thou hast put me to death.'
Absalom ya ce wa Yowab, “Kai, na aika, ‘Ka zo nan don in aike ka wurin sarki ka tambaya, “Me ya sa na dawo daga Geshur? Ai, ya fi mini a ce ina can har yanzu!”’ Yanzu kuwa, ina so in ga sarki, kuma idan na yi wani laifi, to, yă kashe ni.”
33 And Joab cometh unto the king, and declareth [it] to him, and he calleth unto Absalom, and he cometh unto the king, and boweth himself to him, on his face, to the earth, before the king, and the king giveth a kiss to Absalom.
Saboda haka Yowab ya tafi wurin sarki ya gaya masa wannan. Sai sarki ya aika aka zo da Absalom, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa a gaban sarki. Sarki kuwa ya sumbaci Absalom.