< 1 Corinthians 14 >

1 Pursue the love, and seek earnestly the spiritual things, and rather that ye may prophecy,
Ku bi halin ƙauna kuna kuma marmarin neman baye-bayen ruhaniya, musamman baiwar annabci.
2 for he who is speaking in an [unknown] tongue — to men he doth not speak, but to God, for no one doth hearken, and in spirit he doth speak secrets;
Gama duk wanda yake magana da wani harshe ba da mutane yake magana ba, sai dai da Allah. Tabbatacce, ba wanda yake fahimtarsa; yana faɗin asirai ta wurin ruhu ne.
3 and he who is prophesying to men doth speak edification, and exhortation, and comfort;
Amma duk wanda yake annabci, yana magana ne da mutane domin yă gina su, yă ƙarfafa su, yă kuma yi musu ta’aziyya.
4 he who is speaking in an [unknown] tongue, himself doth edify, and he who is prophesying, an assembly doth edify;
Wanda yake magana da wani harshe kuwa, kansa yake gina, amma mai annabci, ikkilisiya ce yake gina.
5 and I wish you all to speak with tongues, and more that ye may prophecy, for greater is he who is prophesying than he who is speaking with tongues, except one may interpret, that the assembly may receive edification.
Zan so kowannenku yă yi magana da harsuna, sai dai zan fi so ku yi annabci. Wanda yake annabci ya fi wanda yake magana da harsuna, sai dai in ya fassara don ikkilisiya ta ginu.
6 And now, brethren, if I may come unto you speaking tongues, what shall I profit you, except I shall speak to you either in revelation, or in knowledge, or in prophesying, or in teaching?
To,’yan’uwa, a ce na zo wurinku ina kuma yin magana da waɗansu harsuna, amfanin me zan yi muku in ban zo muku da wani bayani ko sani ko annabci, ko kuma kalmar koyarwa ba?
7 yet the things without life giving sound — whether pipe or harp — if a difference in the sounds they may not give, how shall be known that which is piped or that which is harped?
Abubuwan nan marasa rai ma da sukan yi ƙara, kamar su algaita ko molo, in muryarsu ba tă fita sosai ba, yaya wani zai san abin da ake busawa ko kaɗawa?
8 for if also an uncertain sound a trumpet may give, who shall prepare himself for battle?
Haka ma in ba a busa ƙaho sosai ba, wa zai yi shirin yaƙi?
9 so also ye, if through the tongue, speech easily understood ye may not give — how shall that which is spoken be known? for ye shall be speaking to air.
Haka yake sa’ad da kuka yi magana da waɗansu harsunan da ba a fahimta. In babu wanda zai san abin da kuke faɗi, za ka dai yi wa iska magana ne kawai.
10 There are, it may be, so many kinds of voices in the world, and none of them is unmeaning,
Ba shakka akwai harsuna iri-iri a duniya, duk da haka kowane a cikinsu yana da ma’ana.
11 if, then, I do not know the power of the voice, I shall be to him who is speaking a foreigner, and he who is speaking, is to me a foreigner;
To, in ban gane ma’anar abin da wani yake faɗi ba, ni baƙo ne ga mai maganar, shi kuma baƙo ne a gare ni.
12 so also ye, since ye are earnestly desirous of spiritual gifts, for the building up of the assembly seek that ye may abound;
Haka yake a gare ku. Da yake kuna marmarin samun baye-bayen ruhaniya, sai ku ba da ƙarfinku ga yin amfani da waɗanda za su gina ikkilisiya.
13 wherefore he who is speaking in an [unknown] tongue — let him pray that he may interpret;
Saboda haka, duk wanda yake magana da harshe, sai yă yi addu’a a yi masa baiwar fassara.
14 for if I pray in an [unknown] tongue, my spirit doth pray, and my understanding is unfruitful.
Gama in na yi addu’a da wani harshe, ruhuna ne yake addu’a, amma tunanina bai amfana kome ba.
15 What then is it? I will pray with the spirit, and I will pray also with the understanding; I will sing psalms with the spirit, and I will sing psalms also with the understanding;
To, me zan yi? Akwai lokutan da zan yi addu’a da ruhuna; akwai kuma lokutan da zan yi addu’a da hankalina. Wani lokaci ya kamata in yi waƙa da ruhuna, a wani lokacin kuma in yi waƙa da hankalina.
16 since, if thou mayest bless with the spirit, he who is filling the place of the unlearned, how shall he say the Amen at thy giving of thanks, since what thou dost say he hath not known?
A cewa waɗansu baƙi suna cikin sujadarku, sa’ad da kuke yabon Allah da ruhunku, yaya waɗanda suke tare ku za su fahimta, har su ce, “Amin,” da yake ba su san abin da kuke faɗi ba?
17 for thou, indeed, dost give thanks well, but the other is not built up!
Ko da yake kuna ba da godiya da kyau, amma wancan mutumin da yake tare da ku bai ginu ba.
18 I give thanks to my God — more than you all with tongues speaking —
Na gode wa Allah, domin ina magana da harsuna fiye da ku duka.
19 but in an assembly I wish to speak five words through my understanding, that others also I may instruct, rather than myriads of words in an [unknown] tongue.
Amma a cikin ikkilisiya zan gwammace in yi magana da kalmomi biyar da za a fahimta don in koyar da waɗansu da a ce in yi magana da kalmomi guda dubu goma a wani harshe.
20 Brethren, become not children in the understanding, but in the evil be ye babes, and in the understanding become ye perfect;
’Yan’uwa, ku daina tunani kamar yara. Wajen mugunta ku zama jarirai, sai dai wajen tunaninku, ku zama manya.
21 in the law it hath been written, that, 'With other tongues and with other lips I will speak to this people, and not even so will they hear Me, saith the Lord;'
A cikin Doka yana a rubuce cewa, “Ta wurin mutane masu baƙin harsuna da kuma ta leɓunan baƙi zan yi magana da waɗannan mutane, amma duk da haka, ba za su saurare ni ba,” in ji Ubangiji.
22 so that the tongues are for a sign, not to the believing, but to the unbelieving; and the prophesy [is] not for the unbelieving, but for the believing,
Harsuna fa alama ce ba ga masu bi ba, sai dai ga marasa bi. Annabci kuwa ga masu bi ne ba ga marasa bi ba.
23 If, therefore, the whole assembly may come together, to the same place, and all may speak with tongues, and there may come in unlearned or unbelievers, will they not say that ye are mad?
Saboda haka, in dukan ikkilisiya ta taru, kowa kuma yana magana da waɗansu harsuna, sai waɗansu jahilai ko waɗansu marasa bi suka shigo, ashe, ba za su ce kuna hauka ba?
24 and if all may prophecy, and any one may come in, an unbeliever or unlearned, he is convicted by all, he is discerned by all,
Amma in wani marar bi, ko jahili ya shigo sa’ad da kowa yana annabci, sai maganar kowa ta ratsa shi, za su shawo kansa yă gane cewa shi mai zunubi ne saboda abin da kowa yake faɗi,
25 and so the secrets of his heart become manifest, and so having fallen upon [his] face, he will bow before God, declaring that God really is among you.
asirin zuciyarsa kuma su bayyana a fili. Don haka, zai fāɗi a ƙasa yă yi wa Allah sujada yana cewa, “Lalle, Allah yana cikinku!”
26 What then is it, brethren? whenever ye may come together, each of you hath a psalm, hath a teaching, hath a tongue, hath a revelation, hath an interpretation? let all things be for building up;
Me za mu ce ke nan’yan’uwa? Sa’ad da kuka taru, wani yakan yi waƙa, wani koyarwa, wani wahayi, wani yin magana da wani harshe, wani kuma fassara. Dole ne a yi duka don gina ikkilisiya.
27 if an [unknown] tongue any one do speak, by two, or at the most, by three, and in turn, and let one interpret;
In kuwa waɗansu za su yi magana a wani harshe, to, kada su fi mutum biyu ko uku, kuma a yi bi da bi, wani kuma yă fassara.
28 and if there may be no interpreter, let him be silent in an assembly, and to himself let him speak, and to God.
In babu mai fassara, sai mai magana yă yi shiru a cikin ikkilisiya, yă yi wa kansa magana da kuma Allah.
29 And prophets — let two or three speak, and let the others discern,
Annabawa biyu ko uku za su iya yin magana, sauran kuma sai su auna a hankali abin da aka faɗa.
30 and if to another sitting [anything] may be revealed, let the first be silent;
In kuma wahayi ya zo wa wani da yake zaune, sai mai magana na farko yă yi shiru.
31 for ye are able, one by one, all to prophesy, that all may learn, and all may be exhorted,
Dukanku kuna iya yin annabci bi da bi, domin kowa yă sami koyarwa da ƙarfafawa.
32 and the spiritual gift of prophets to prophets are subject,
Ruhohin annabawa kuwa suna ƙarƙashin sarrafawar annabawa.
33 for God is not [a God] of tumult, but of peace, as in all the assemblies of the saints.
Gama Allah, ba Allah mai sa rikicewa ba ne, sai dai mai salama. Kamar yadda yake a dukan ikkilisiyoyi na tsarkaka.
34 Your women in the assemblies let them be silent, for it hath not been permitted to them to speak, but to be subject, as also the law saith;
Ya kamata mata su zauna shiru a cikin ikkilisiyoyi. Ba su da izinin yin magana, sai dai su yi biyayya yadda Doka ta faɗi.
35 and if they wish to learn anything, at home their own husbands let them question, for it is a shame to women to speak in an assembly.
In suna so su yi tambaya game da wani abu, ya kamata su tambayi mazansu a gida, domin abin kunya ne mace tă yi magana a cikin ikkilisiya.
36 From you did the word of God come forth? or to you alone did it come?
Shin, a kanku ne maganar Allah ta fara? Ko kuma a gare ku ne kaɗai ta iso?
37 if any one doth think to be a prophet, or spiritual, let him acknowledge the things that I write to you — that of the Lord they are commands;
In wani yana tsammani shi annabi ne, ko yana da baiwar ruhaniya, bari yă gane cewa abin da nake rubuta muku umarnin Ubangiji ne.
38 and if any one is ignorant — let him be ignorant;
In ya ƙi kula da wannan, shi ma sai a ƙi kula da shi.
39 so that, brethren, earnestly desire to prophesy, and to speak with tongues do not forbid;
Saboda haka’yan’uwana, ku yi marmarin yin annabci, kada kuma ku hana magana da harsuna.
40 let all things be done decently and in order.
Sai dai a yi kome daidai da kuma cikin tsari.

< 1 Corinthians 14 >