< 1 Chronicles 24 >
1 And to the sons of Aaron [are] their courses: sons of Aaron [are] Nadab, and Abihu, Eleazar, and Ithamar,
Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
2 and Nadab dieth, and Abihu, in the presence of their father, and they had no sons, and Eleazar and Ithamar act as priests.
Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
3 And David distributeth them, and Zadok of the sons of Eleazar, and Ahimelech of the sons of Ithamar, according to their office in their service;
Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
4 and there are found of the sons of Eleazar more for heads of the mighty men than of the sons of Ithamar; and they distribute them: Of the sons of Eleazar, heads for a house of fathers, sixteen; and of the sons of Ithamar, for a house of their fathers, eight.
Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
5 And they distribute them, by lots, one with another, for princes of the sanctuary, and princes of God, have been of the sons of Eleazar, and of the sons of Ithamar.
Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
6 And Shemaiah son of Nethaneel the scribe, of the Levites, writeth them before the king and the princes, and Zadok the priest, and Ahimelech son of Abiathar, and heads of the fathers, for priests and for Levites: one house of a father being taken possession of for Eleazar, and one being taken possession of for Ithamar.
Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
7 And the first lot goeth out for Jehoiarib, for Jedaiah the second,
Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
8 for Harim the third, for Seorim the fourth,
na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
9 for Malchijah the fifth, for Mijamin the sixth,
na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
10 for Hakkoz the seventh, for Abijah the eighth,
na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
11 for Jeshuah the ninth, for Shecaniah the tenth,
na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
12 for Eliashib the eleventh, for Jakim the twelfth,
na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
13 for Huppah the thirteenth, for Jeshebeab the fourteenth,
na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
14 for Bilgah the fifteenth, for Immer the sixteenth,
na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
15 for Hezir the seventeenth, for Aphses the eighteenth,
na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
16 for Pethahiah the nineteenth, for Jehezekel the twentieth,
na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
17 for Jachin the one and twentieth, for Gamul the two and twentieth,
na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
18 for Delaiah the three and twentieth, for Maaziah the four and twentieth.
na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
19 These [are] their appointments for their service, to come in to the house of Jehovah, according to their ordinance by the hand of Aaron their father, as Jehovah God of Israel, commanded them.
Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
20 And for the sons of Levi who are left: for sons of Amram, Shubael; for sons of Shubael: Jehdeiah.
Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
21 For Rehabiah: for sons of Rehabiah, the head Ishshiah.
Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
22 For the Izharite: Shelomoth; for sons of Shelomoth: Jahath.
Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
23 And sons of Jeriah: Amariah the second, Jahaziel the third, Jekameam the fourth.
’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
24 Sons of Uzziel: Michah; for sons of Michah: Shamir.
Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
25 A brother of Michah [is] Ishshiah; for sons of Ishshiah: Zechariah;
Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
26 sons of Merari: Mahli and Mushi; sons of Jaaziah: Beno;
’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
27 sons of Merari: of Jaaziah: Beno, and Shoham, and Zaccur, and Ibri.
’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
28 For Mahli: Eleazar, who had no sons;
Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
29 for Kish: sons of Kish: Jerahmeel.
Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
30 And sons of Mushi [are] Mahli, and Eder, and Jerimoth; these [are] sons of the Levites, for the house of their fathers,
Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
31 and they cast, they also, lots over-against their brethren the sons of Aaron, before David the king, and Zadok, and Ahimelech, and heads of the fathers, for priests and for Levites; the chief father over-against his younger brother.
Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.