< Zephaniah 1 >

1 The word of the Lord, that was maad to Sofonye, sone of Chusi, sone of Godolie, sone of Amasie, sone of Ezechie, in the daies of Josie, the sone of Amon, king of Juda.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 Y gaderinge schal gadere alle thingis fro the face of erthe, seith the Lord;
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 Y gaderynge man and beeste, Y gaderynge volatils of heuene, and fischis of the see; and fallyngis of vnpitouse men schulen be, and Y schal leese men fro face of erthe, seith the Lord.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 And Y schal stretche out myn hond on Juda, and on alle dwellers of Jerusalem; and Y schal lese fro this place the relifs of Baal, and the names of keperis of housis, with prestis;
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 and hem that worschipen on roouys the knyythod of heuene, and worschipen, and sweren in the Lord, and sweren in Melchon;
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 and whiche ben turned awei bihynde the bak of the Lord, and whiche `souyten not the Lord, nether enserchiden hym.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Be ye stille fro the face of the Lord God, for niy is the dai of the Lord; for the Lord made redi a sacrifice, halewide hise clepid men.
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 And it schal be, in the dai of sacrifice of the Lord, Y schal visite on princes, and on sones of the kyng, and on alle that ben clothid with pilgrimys, ether straunge, clothing.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 And Y schal visite on ech that proudli entrith on the threisfold in that dai, whiche fillen the hous of her Lord God with wickidnesse and gile.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 And ther schal be in that dai, seith the Lord, a vois of cry fro the yate of fischis, and yellynge fro the secounde yate, and greet defoulyng fro litle hillis.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Yelle ye, dwelleris of Pila; al the puple of Canaan was stille togidere, alle men wlappid in siluer perischiden.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 And it schal be, in that tyme Y schal seke Jerusalem with lanternes, and Y schal visite on alle men piyt in her darstis, whiche seien in her hertis, The Lord schal not do wel, and he schal not do yuele.
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 And the strengthe of hem schal be in to rauyschyng, and the housis of hem in to desert; and thei schulen bilde housis, and schulen not enhabite; and thei schulen plaunte vyneyerdis, and thei schulen not drynke the wyn of hem.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 Nyy is the greet dai of the Lord, niy and swift ful myche; the vois of the dai of the Lord is bittir, a strong man schal be in tribulacioun there.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 `The ilke dai is a dai of wraththe, dai of tribulacioun and angwisch, dai of nedynesse and wretchidnesse, dai of derknessis and myist, dai of cloude and whirlewynd,
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 dai of trumpe and noise on strong citees and on hiye corneris.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 And Y schal troble men, and thei schulen walke as blynde, for thei han synned ayens the Lord; and the blood of hem schal be sched out as erthe, and the bodies of hem schulen be as tordis.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 But and the siluer of hem, and gold of hem, schal not mowe delyuere hem in the dai of wraththe of the Lord; in fier of his feruour al erthe schal be deuourid, for he schal make ende with haastyng to alle men enhabitynge the erthe.
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.

< Zephaniah 1 >