< Zechariah 1 >

1 In the eiythe monethe, in the secounde yeer of Darius, the word of the Lord was maad to Sacarie, the sone of Barachie, the sone of Addo,
A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
2 profete, and seide, The Lord is wrooth on youre fadris with wrathfulnesse.
“Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
3 And thou schalt seie to hem, The Lord of oostis seith these thingis. Be ye conuertid to me, seith the Lord of oostis, and Y schal be conuertid to you, seith the Lord of oostis.
Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Be ye not as youre fadris, to whiche the formere profetis crieden, seiynge, The Lord of oostis seith these thingis, Be ye conuertid fro youre yuel weies, and youre worste thouytis; and thei herden not, nether token tent to me, seith the Lord of oostis.
Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
5 Where ben youre fadris and profetis? whether thei schulen lyue with outen ende?
Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
6 Netheles my wordis and my lawful thingis, whiche Y comaundide to my seruauntis profetis, whether thei tauyten not youre fadris? And thei weren conuertid, and seiden, As the Lord of oostys thouyte for to do to vs bi oure weies, and bi oure fyndingis he dide to vs.
Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
7 In the foure and twentithe dai of the enleuenthe monethe Sabath, in the secounde yeer of Darius, the word of the Lord was maad to Sacarie, sone of Barachie, sone of Addo,
A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
8 profete, and seide, Y saiy bi niyt, and lo! a man stiynge on a reed hors; and he stood bitwixe places where mirtis wexen, that weren in the depthe, and aftir hym weren horsis reede, dyuerse, and white.
Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
9 And Y seide, My lord, who ben these? And an aungel of the Lord seide to me, that spak in me, Y schal schewe to thee what these ben.
Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
10 And the man that stood bitwix places where mirtis wexen, answeride, and seide, These it ben, whiche the Lord sente, that thei walke thorouy erthe.
Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
11 And thei answeriden to the aungel of the Lord, that stood bitwixe places where mirtis wexen, and seiden, We han walkid thorouy erthe, and lo! al erthe is enhabitid, and restith.
Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
12 And the aungel of the Lord answeride, and seide, Lord of oostis, hou long schalt thou not haue merci on Jerusalem, and citees of Juda, to whiche thou art wrooth? This now is the seuentithe yeer.
Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
13 And the Lord answeride to the aungel, that spak in me, goode wordis, and wordis of coumfort.
Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
14 And the aungel that spak in me, seide to me, Crie thou, seiynge, The Lord of oostis seith these thingis, Y louyde Jerusalem and Sion in greet feruour;
Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
15 and in greet wraththe Y schal be wroth on riche folkis; for Y was wrooth a litil, forsothe thei helpiden in to yuel.
amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
16 Therfor the Lord seith these thingis, Y schal turne ayen to Jerusalem in mercies. Myn hous schal be bildid in it, seith the Lord of oostis; and a plomet schal be streiyt out on Jerusalem.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
17 Yit crie thou, seiynge, The Lord of oostis seith these thingis, Yit my citees schulen flete with goodis, and yit the Lord schal coumforte Sion, and yit he schal chese Jerusalem.
“Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
18 And Y reiside myn iyen, and Y saiy, and lo! foure hornes.
Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
19 And Y seide to the aungel that spak in me, What ben these? And he seide to me, These ben hornes, that wyndewiden Juda, and Israel, and Jerusalem.
Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
20 And the Lord schewide to me foure smythis.
Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
21 And Y seide, What comen these for to do? Which spak, seiynge, These ben the hornes, that wyndewiden Juda bi alle men, and no man of hem reiside his heed; and these camen for to make hem aferd, that thei caste doun the hornes of hethene men, which reisiden horn on the lond of Juda, for to scatere it.
Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”

< Zechariah 1 >