< Ruth 1 >

1 In the daies of o iuge, whanne iugis weren souereynes, hungur was maad in the lond; and a man of Bethleem of Juda yede to be a pylgrym in the cuntrei of Moab, with his wijf and twey fre sones.
A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
2 He was clepid Elymelech, and his wijf Noemy, and the twey sones, `the oon was clepid Maalon, and the tother Chelion, Effrateis of Bethleem of Juda; and thei entriden in to the cuntrey of Moab, and dwelliden there.
Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
3 And Elymelech, the hosebonde of Noemy, diede, and sche lefte with the sones;
To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
4 and thei token wyues of Moab, of whiche wyues oon was clepid Orpha, the tother Ruth. And the sones dwelliden there ten yeer,
Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
5 and bothe dieden, that is, Maalon and Chelion; and the womman lefte, and was maad bare of twey fre sones, and hosebonde.
sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
6 And sche roos to go with euer eithir wijf of hir sones in to hir cuntrey fro the cuntrey of Moab; for sche hadde herd, that the Lord hadde biholde his puple, and hadde youe `metis to hem.
Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
7 Therfor sche yede out of the place of hir pilgrymage with euer either wijf of hir sones; and now sche was set in the weie of turnyng ayen in to the lond of Juda,
Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
8 and sche seide to hem, Go ye in to `the hows of youre modir; the Lord do mercy with you, as ye diden with the deed men, and with me;
Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
9 the Lord yyue to you to fynde reste in the howsis of hosebondis, whiche ye schulen take. And sche kiste hem. Whiche bigunnen to wepe with `vois reisid,
Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
10 and to seie, We schulen go with thee to thi puple.
suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
11 To whiche sche answeride, My douytris, turne ye ayen, whi comen ye with me? Y haue no more sones in my wombe, that ye moun hope hosebondis of me; my douytris of Moab, turne ye ayen, and go;
Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
12 for now Y am maad eeld, and Y am not able to boond of mariage; yhe, thouy Y myyte conseyue in this nyyt,
Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
13 and bere sones, if ye wolen abide til thei wexen, and fillen the yeris of mariage, `ye schulen sunner be eld wymmen than ye schulen be weddid; I biseche, `nyle ye, my douytris, for youre angwische oppressith me more, and the hond of the Lord yede out ayens me.
za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
14 Therfor, whanne the vois was reisid, eft thei bigunnen to wepe. Orpha kisside `the modir of hir hosebonde, and turnede ayen, and Ruth `cleuyde to `the modir of hir hosebonde.
A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
15 To whom Noemy seide, Lo! thi kyneswomman turnede ayen to hir puple, and to hir goddis; go thou with hir.
Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
16 And sche answeride, Be thou not `aduersarye to me, that Y forsake thee, and go awei; whidur euer thou schalt go, Y schal go, and where thou schalt dwelle, and Y schal dwelle togidere; thi puple is my puple, and thi God is my God;
Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
17 what lond schal resseyue thee diynge, Y schal die ther ynne, and there Y schal take place of biriyng; God do to me these thingis, and adde these thingis, if deeth aloone schal not departe me and thee.
Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
18 Therfor Noemy siy, that Ruth hadde demyde with stidefast soule to go with hir, and sche nolde be ayens hir, nether counseile ferthere turnynge ayen `to her cuntrei men.
Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
19 And thei yeden forth togidere, and camen in to Bethleem; and whanne thei entriden in to the citee, swift fame roos anentis alle men, and wymmen seiden, This is thilke Noemy.
Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
20 To whiche sche seide, Clepe ye not me Noemy, that is, fair, but `clepe ye me Mara, that is, bittere; for Almyyti God hath fillid me greetli with bitternesse.
Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
21 Y yede out ful, and the Lord ledde me ayen voide; whi therfor clepen ye me Noemy, whom the Lord hath `maad low, and Almyyti God hath turmentid?
In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
22 Therfor Noemy cam with Ruth of Moab, `the wijf of hir sone, fro the lond of hir pilgrimage, and turnede ayen in to Bethleem, whanne barli was ropun first.
Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.

< Ruth 1 >