< Romans 1 >

1 Poul, the seruaunt of Jhesu Crist, clepid an apostle, departid in to the gospel of God;
Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah.
2 which he hadde bihote tofore bi his profetis in holi scripturis of his sone,
Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa.
3 which is maad to hym of the seed of Dauid bi the flesch,
Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.
4 and he was bifor ordeyned the sone of God in vertu, bi the spirit of halewyng of the ayenrisyng of deed men, of Jhesu Crist oure Lord,
Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu.
5 bi whom we han resseyued grace and the office of apostle, to obeie to the feith in alle folkis for his name,
Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa.
6 among whiche ye ben also clepid of Jhesu Crist,
cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
7 to alle that ben at Rome, derlyngis of God, and clepid hooli, grace to you, and pees of God oure fadir, and of the Lord Jhesu Crist.
Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
8 First Y do thankyngis to my God, bi Jhesu Crist, for alle you, for youre feith is schewid in al the world.
Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya.
9 For God is a witnesse to me, to whom Y serue in my spirit, in the gospel of his sone,
Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku.
10 that with outen ceessyng Y make mynde of you euere in my preieris, and biseche, if in ony maner sum tyme Y haue a spedi weie in the wille of God to come to you.
A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
11 For Y desire to se you, to parten sumwhat of spiritual grace,
Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku.
12 that ye be confermyd, that is, to be coumfortid togidere in you, bi feith that is bothe youre and myn togidere.
Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
13 And, britheren, Y nyle, that ye vnknowun, that ofte Y purposide to come to you, and Y am lett to this tyme, that Y haue sum fruyt in you, as in othere folkis.
Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai.
14 To Grekis and to barberyns, to wise men and to vnwise men,
Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima.
15 Y am dettour, so that that is in me is redi to preche the gospel also to you that ben at Rome.
Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
16 For Y schame not the gospel, for it is the vertu of God in to heelthe to ech man that bileueth, to the Jew first, and to the Greke.
Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,
17 For the riytwisnesse of God is schewid in it, of feith in to feith,
Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, “Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya.”
18 as it is writun, For a iust man lyueth of feith. For the wraththe of God is schewid fro heuene on al vnpite and wickidnesse of tho men, that withholden the treuthe of God in vnriytwisnes.
Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su.
19 For that thing of God that is knowun, is schewid to hem, for God hath schewid to hem.
Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
20 For the vnuysible thingis of hym, that ben vndurstondun, ben biholdun of the creature of the world, bi tho thingis that ben maad, yhe, and the euerlastynge vertu of hym and the godhed, so that thei mowe not be excusid. (aïdios g126)
Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. (aïdios g126)
21 For whanne thei hadden knowe God, thei glorifieden hym not as God, nether diden thankyngis; but thei vanyschiden in her thouyts, and the vnwise herte of hem was derkid.
Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
22 For thei `seiynge that hem silf weren wise, thei weren maad foolis.
Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye.
23 And thei chaungiden the glorie of `God vncorruptible in to the licnesse of an ymage of a deedli man, and of briddis, and of foure footid beestis, and of serpentis.
Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
24 For which thing God bitook hem in to the desiris of her herte, in to vnclennesse, that thei punysche with wrongis her bodies in hem silf.
Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu.
25 The whiche chaungiden the treuthe of God in to leesyng, and herieden and serueden a creature rathere than to the creatoure, that is blessid in to worldis of worldis. (aiōn g165)
Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
26 Amen. Therfor God bitook hem in to passiouns of schenschipe. For the wymmen of hem chaungiden the kyndli vss in to that vss that is ayens kynde.
Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace.
27 Also the men forsoken the kyndli vss of womman, and brenneden in her desiris togidere, and men in to men wrouyten filthehed, and resseyueden in to hem silf the meede that bihofte of her errour.
Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
28 And as thei preueden that thei hadden not God in knowyng, God bitook hem in to a repreuable wit, that thei do tho thingis that ben not couenable; that thei ben fulfillid with al wickidnesse,
Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
29 malice, fornycacioun, coueitise, weiwardnesse, ful of enuye, mansleyngis, strijf, gile, yuel wille, preuy bacbiteris, detractouris,
Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi.
30 hateful to God, debateris, proude, and hiy ouer mesure, fynderis of yuele thingis, not obeschynge to fadir and modir,
Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu.
31 vnwise, vnmanerli, withouten loue, withouten boond of pees, with outen merci.
Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
32 The whiche whanne thei hadden knowe the riytwisnesse of God, vndirstoden not, that thei that don siche thingis ben worthi the deth, not oneli thei that don tho thingis, but also thei that consenten to the doeris.
Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.

< Romans 1 >