< Revelation 2 >

1 And to the aungel of the chirche of Efesus write thou, These thingis seith he, that holdith the seuene sterris in his riyt hond, which walkith in the middil of the seuene goldun candilstikis.
''Zuwa ga mala'ikan dake ikilisiyar Afisus, ka rubuta: 'Wadannan sune kalmomin wanda ke rike da taurari bakwai a cikin hannun damarsa. wanda yake tafiya a tsakanin zankayen fitilun zinari bakwai,
2 Y woot thi werkis, and trauel, and thi pacience, and that thou maist not suffre yuele men; and thou hast asaied hem that seien that thei ben apostlis, and ben not, and thou hast foundun hem lieris;
''Na san abubuwan da ka yi, da famar ka, da hakurinka da jimirinka. Na sani ba ka jimrewa miyagun mutane, na sani ka gwada wadanda suka ce da kansu, su manzanni ne, amma ba haka ba, ka tarar da su makaryata.
3 and thou hast pacience, and thou hast suffrid for my name, and failidist not.
Na san kana da tsawon jimrewa, kuma ka sha wahala sosai sabili da sunana, kuma baka gaji ba.
4 But Y haue ayens thee a fewe thingis, that thou hast left thi firste charite.
Amma ga rashin jin dadi na da kai, ka bar kaunar ka ta fari.
5 Therfor be thou myndeful fro whennus thou hast falle, and do penaunce, and do the firste werkis; ether ellis, Y come soone to thee, and Y schal moue thi candilstike fro his place, but `thou do penaunce.
Domin haka ka tuna daga inda ka fadi. Ka tuba ka yi abubuwan da ka yi da fari. Sai fa ka tuba, zan zo maka in kuma cire fitilar ka daga mazauninta.
6 But thou hast this good thing, that thou hatidist the dedis of Nycholaitis, the whiche also Y hate.
Amma kana da wannan: Ka tsani abubuwan da Nikolatawa suka yi, wanda nima na tsana.
7 He that hath eeris, here he, what the spirit seith to the chirchis. To hym that ouercometh Y schal yyue to ete of the tre of lijf, that is in the paradis of my God.
wanda yake da kunnen ji ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bashi dama ya ci daga itacen rai, wanda ke cikin firdausin Allah.””
8 And to the aungel of the chirche of Smyrma write thou, These thingis seith the firste and the laste, that was deed, and lyueth.
Zuwa ga mala'ikan da ke Ikilisiliyar Samirna rubuta: 'Wadannan su ne kalmomin wanda yake shine farko shine karshe, wanda ya mutu ya sake rayuwa kuma.
9 Y woot thi tribulacioun, and thi pouert, but thou art riche; and thou art blasfemyd of hem, that seien, that thei ben Jewis, and ben not, but ben the synagoge of Sathanas.
''Na san wahalun ka da talaucin ka amma kana da arziki. Nasan masu bata suna wadanda suke cewa su Yahudawa ne, amma ba haka suke ba. Su majami'ar Shaidan ne.
10 Drede thou no thing of these thingis, whiche thou schalt suffre. Lo! the deuel schal sende summe of you in to prisoun, that ye be temptid; and ye schulen haue tribulacioun ten daies. Be thou feithful to the deth, and Y schal yyue to thee a coroun of lijf.
Kada ka ji tsoron wahalar da zaka fuskanta nan gaba. Duba! Shaidan yana gab da jefa wadansun ku cikin kurkuku, domin a gwada ku, kuma zaku sha wahala ta kwana goma. Kuyi aminci har ga mutuwa zan baku rawanin rai.
11 He that hath eeris, here he, what the spirit seith to the chirchis. He that ouercometh, schal not be hirt of the secounde deth.
wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Shi wanda yayi nasara ba zai cutu a mutuwa ta biyu ba.””
12 And to the aungel of the chirche of Pergamus write thou, These thingis seith he, that hath the swerd scharp on ech side.
''Zuwa ga mala'ikan dake ikilisiyar Burgamas rubuta: 'Wadannan ne kalmomin wanda ya ke da takobi mai kaifi biyu;
13 Y woot where thou dwellist, where the seete of Sathanas is; and thou holdist my name, and denyedist not my feith. And in tho daies was Antifas, my feithful witnesse, that was slayn at you, where Sathanas dwellith.
''Na san inda kake zama can inda kursiyin shaidan yake. Duk da haka ka rike sunana da karfi, na sani baka yi musun bangaskiyar ka da ni ba, ko a lokacin Antifas mashaidina, amintaccena, wanda aka kashe a tsakaninku, can inda shaidan yake zama.
14 But Y haue ayens thee a fewe thingis; for thou hast `there men holdinge the teching of Balaam, which tauyte Balaac for to sende sclaundre bifor the sones of Israel, to ete of sacrificis of ydols, and to do fornicacioun;
Amma ga rashin jin dadi na kadan da kai: Kana da wadansu da suke rike da koyarwar Bil'amu kamkam, wanda ya koya wa Balak ya sa abin tuntubi gaban 'ya'yan Isra'ila, domin su ci abincin da aka mika wa gumaka kuma suyi fasikanci.
15 so also thou hast men holdinge the teching of Nycholaitis.
Hakannan kuma wasunku sun rike koyarwar Nikolatawa kamkam.
16 Also do thou penaunce; `yif ony thing lesse, Y schal come soone to thee, and Y schal fiyte with hem with the swerd of my mouth.
Sabili da haka ka tuba! Idan ka ki zan zo gare ka da sauri, kuma in yi yaki gaba da su da takobi dake cikin bakina.
17 He that hath eeris, here he, what the spirit seith to the chirches. To him that ouercometh Y schal yyue aungel mete hid; and Y schal yyue to hym a whiit stoon, and in the stoon a newe name writun, which no man knowith, but he that takith.
Bari wanda yake da kunne ya sauriri abin da Ruhu yake fadawa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bada wata boyayyar manna, kuma zan bashi farin dutse da sabon suna a rubuce a kan dutsen, suna wanda ba wanda ya sani, sai shi wanda ya karbe shi.””
18 And to the aungel of the chirche of Tiatira write thou, These thingis seith the sone of God, that hath iyen as flawme of fier, and hise feet lijk latoun.
Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Tiyatira rubuta: 'Wadannan sune kalamomin Dan Allah, wanda yake da idanu kamar harshen wuta; sawayen kamar gogaggiyar tagulla:
19 Y knowe thi werkis, and feith, and charite, and thi seruyce, and thi pacience, and thi laste werkis mo than the formere.
''Na san abin da ka yi, kaunar ka, da bangaskiya da hidima da tsawon jimrewar ka. Na san abinda ka yi bada dadewa ba ya fi abinda ka yi da fari.
20 But Y haue ayens thee a fewe thingis; for thou suffrist the womman Jesabel, which seith that sche is a prophetesse, to teche and disseyue my seruauntis, to do letcherie, and to ete of thingis offrid to idols.
Amma ga rashin jin dadi na da kai: Kana hakurce wa matar nan Yezebel, wadda take kiran kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta, ta rudi bayina suyi fasikanci kuma su ci abincin da aka mika wa gumaka sadaka.
21 And Y yaf to hir time, that sche schulde do penaunce, and sche wolde not do penaunce of hir fornycacioun.
Na bata lokaci domin ta tuba amma bata so ta tuba da fasikancin ta.
22 And lo! Y sende hir in to a bed, and thei that doen letcherie with hir schulen be in moost tribulacioun, but thei don penaunce of hir werkis.
Duba! zan jefa ta a kan gadon jinya, wadanda kuma suka yi zina da ita za su shiga babbar wahala, sai dai in sun tuba daga ayukan ta.
23 And Y schal slee hir sones in to deth, and alle chirchis schulen wite, that Y am serchinge reynes and hertis; and Y schal yyue to ech man of you after hise werkis.
Zan buga 'ya'yanta da mutuwa, kuma dukan ikilisiyoyi zasu san cewa nine wanda nake bincike tunani da zukata. Zan ba kowanen ku bisa ga ayyukansa.
24 And Y seie to you, and to othere that ben at Tiatire, who euer han not this teching, and that knewen not the hiynesse of Sathanas, hou thei seien, Y schal not sende on you another charge; netheles holde ye that that ye han,
Amma ga sauran ku dake cikin Tayatira, ga kowanen ku wanda bai rike wannan koyarwar ba, kuma bai san abinda wadansu suke kira zurfafan abubuwan Shaidan ba—ga ku na ce ban sa muku wata nawaya ba.'
25 til Y come.
Duk da haka dole ku tsaya da karfi har in zo.
26 And to hym that schal ouercome, and that schal kepe til in to the ende my werkis, Y schal yyue power on folkis,
Wanda yayi nasara da wanda ya yi abin da na yi har karshe, a gareshi zan bada iko akan al'ummai
27 and he schal gouerne hem in an yrun yerde; and thei schulen be brokun to gidre,
Zai yi mulkin su da sandar karfe, zai farfasa su kamar randunan yumbu.”
28 as a vessel of a pottere, as also Y resseyuede of my fadir; and Y schal yyue to hym a morewe sterre.
Kamar yadda na karba daga wurin Ubana, ni kuma zan bashi tauraron asubahi.
29 He that hath eeris, here he, what the spirit seith to the chirchis.
Bari wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fadawa ikilisiyioyi.””

< Revelation 2 >