< Revelation 11 >

1 And a reed lijk a yerde was youun to me, and it was seid to me, Rise thou, and meete the temple of God, and the auter, and men that worschipen in it.
Aka bani sanda in yi amfani da ita kamar sandar awo. Aka ce mani, “Tashi ka auna haikalin Allah da bagadi, da wadanda ke sujada a cikinsa.
2 But caste thou out the foryerd, that is with out the temple, and mete not it; for it is youun to hethene men, and thei schulen defoule the hooli citee bi fourti monethis and tweyne.
Amma kada ka auna harabar haikalin, domin an ba da shi ga Al'ummai. Za su tattake birnin mai tsarki har wata arba'in da biyu.
3 And Y schal yyue `to my twey witnessis, and thei schulen prophesie a thousynde daies two hundrid and sixti, and schulen be clothid with sackis.
Zan ba shaidu na biyu iko su yi anabci na kwanaki dubu daya da dari biyu da sittin, sanye da tsummoki.
4 These ben tweyne olyues, and twei candilstikis, and thei stonden in the siyt of the Lord of the erthe.
Wadannan shaidu sune itatuwan zaitun biyu da kuma fitilu biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
5 And if ony man wole anoye hem, fier schal go out of the mouth of hem, and schal deuoure her enemyes. And if ony wole hirte hem, thus it bihoueth hym to be slayn.
Idan wani ya yi niyyar cutar da su, wuta na fitowa daga bakinsu ta lashe makiyansu. Duk mai son cutar da su, dole a kashe shi ta wannan hanya.
6 These han power to close heuene, that it reyne not in the daies of her prophesie; and thei han power on watris, to turne hem in to blood; and to smyte the erthe with euery plage, and as ofte as thei wolen.
Wadannan shaidu suna da iko su kulle sama domin kada a yi ruwa a lokacin da suke anabci. Suna da iko su juya ruwaye su zama jini, su kuma bugi duniya da kowacce irin annoba duk lokacin da suka ga dama.
7 And whanne thei schulen ende her witnessing, the beeste that stieth vp fro depnesse, schal make batel ayens hem, and schal ouercome hem, and schal sle hem. (Abyssos g12)
Sa'adda suka gama shaidarsu, dabban da ke fitowa daga rami marar iyaka zai yi yaki da su. Zai ci nasara da su ya kashe su. (Abyssos g12)
8 And the bodies of hem schulen ligge in the stretis of the greet citee, that is clepid goostli Sodom, and Egipt, where the Lord of hem was crucified.
Gawawwakinsu zasu kwanta kan hanyar babban birnin nan (wanda ma'anar sa ake kira Saduma da Masar) inda aka gicciye Ubangijinsu.
9 And summe of lynagis, and of puplis, and of langagis, and of hethene men, schulen se the bodies of hem bi thre daies and an half; and thei schulen not suffre the bodies of hem to be put in biriels.
Wajen kwana uku da rabi wadansu daga dukan mutane, da kabila, da harshe, da al'umma za su yi kallon gawawwakinsu. Za su ki yarda a sa su cikin kabari.
10 And men enhabitynge the erthe schulen haue ioye on hem; and thei schulen make myrie, and schulen sende yiftis togidere, for these twei prophetis turmentiden hem that dwellen on the erthe.
Mazaunan duniya zasu yi murna da biki a kansu. Har za su aika wa juna kyautai saboda annabawan nan biyu da suka azabtar da mazaunan duniya.
11 And aftir thre daies and an half, the spirit of lijf of God entride in to hem; and thei stoden on her feet, and greet dreed felle on hem that sayn hem.
Amma bayan kwana uku da rabi, numfanshin rai daga wurin Allah zai shiga cikinsu sa'annan za su tsaya a kan kafafunsu. Matsanancin tsoro zata fado kan wadanda za su gansu.
12 And thei herden a greet vois fro heuene, seiynge to hem, Come vp hidir. And thei stieden in to heuene in a cloude, and the enemyes of hem sayn hem.
Sa'annan zasu ji murya mai kara daga sama tana ce masu, “Ku hauro nan!” Sa'annan za su tafi sama cikin gajimarai, makiyansu suna kallo.
13 And in that our a greet erthe mouyng was maad, and the tenthe part of the citee felle doun; and the names of men seuene thousynde weren slayn in the erthe mouyng; and the tother weren sent in to drede, and yauen glorie to God of heuene.
A waccan sa'a za a yi babbar girgizar kasa, sai kashi daya cikin goma na garin ya fadi. Mutane dubu bakwai za su mutu a girgizar kasar, wadanda suka tsira kuwa za su tsorata su ba da daukaka ga Allah na sama.
14 The secounde wo is gon, and lo! the thridde wo schal come soone.
Annoba ta biyu ta wuce. Duba! Annoba ta uku tana zuwa nan da nan.
15 And the seuenthe aungel trumpide, and grete voicis weren maad in heuene, and seiden, The rewme of this world is maad `oure Lordis, and of Crist, his sone; and he schal regne in to worldis of worldis. (aiōn g165)
Sa'annan mala'ika na bakwai ya busa kahonsa, sai muryoyi masu kara suka yi magana cikin sama cewa, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Almasihunsa. Zai yi mulki har abada abadin.” (aiōn g165)
16 Amen. And the foure and twenti eldre men, that saten in her seetis in the siyt of the Lord, fellen on her faces, and worschipiden God,
Sa'annan dattawan nan ashirin da hudu da ke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fadi fuskokinsu na kasa. Suka yi wa Allah sujada.
17 and seiden, We don thankyngis to thee, Lord God almyyti, which art, and which were, and which art to comynge; which hast takun thi greet vertu, and hast regned.
Suka ce, “Mun yi maka godiya, Ubangiji Allah, Madaukaki, wanda yake yanzu da wanda yake a da, saboda ka dauki ikonka mai girma ka fara mulki.
18 And folkis ben wrooth, and thi wraththe cam, and tyme of dede men to be demyd, and to yelde mede to thi seruauntis, and prophetis, and halewis, and dredynge thi name, to smale and to grete, and to distrie hem that corrumpiden the erthe.
Al'ummai suka fusata, amma hasalar ka ta zo. Lokaci ya zo da za a yi wa mattatu sharia, da zaka ba da sakamako ga bayinka annabawa, da masu ba da gaskiya, da wadanda suka ji tsoron sunanka, karami da babba. Lokaci kuma ya yi da za ka hallaka wadanda ke hallakar da duniya.”
19 And the temple of God in heuene was openyd, and the arke of his testament was seyn in his temple; and leityngis weren maad, and voices, and thondris, and `erthe mouyng, and greet hail.
Sa'annan aka bude haikalin Allah da ke sama, sai aka ga akwatin alkawarinsa a cikin haikalinsa. Sai ga hasken walkiya, da rugugi, da aradu, da girgizar kasa, da manyan duwatsun kankara.

< Revelation 11 >