< Psalms 88 >

1 The song of salm, to the sones of Chore, to victorie on Mahalat, for to answere, the lernyng of Heman Ezraite. Lord God of myn helthe; Y criede in dai and nyyt bifore thee.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Mi preier entre bifore thi siyt; bowe doun thin eere to my preier.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 For my soule is fillid with yuels; and my lijf neiyede to helle. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 I am gessid with hem that goon doun in to the lake; Y am maad as a man with outen help,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 and fre among deed men. As men woundid slepinge in sepulcris, of whiche men noon is myndeful aftir; and thei ben put awei fro thin hond.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Thei han put me in the lower lake; in derke places, and in the schadewe of deth.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Thi strong veniaunce is confermed on me; and thou hast brouyt in alle thi wawis on me.
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Thou hast maad fer fro me my knowun; thei han set me abhomynacioun to hem silf. I am takun, and Y yede not out;
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 myn iyen weren sijk for pouert. Lord, Y criede to thee; al dai Y spredde abrood myn hondis to thee.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Whethir thou schalt do merueils to deed men; ether leechis schulen reise, and thei schulen knouleche to thee?
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Whether ony man in sepulcre schal telle thi merci; and thi treuthe in perdicioun?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Whether thi merueilis schulen be knowun in derknessis; and thi riytfulnesse in the lond of foryetyng?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 And, Lord, Y criede to thee; and erli my preier schal bifor come to thee.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Lord, whi puttist thou awei my preier; turnest awei thi face fro me?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 I am pore, and in traueils fro my yongthe; sotheli Y am enhaunsid, and Y am maad low, and disturblid.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Thi wraththis passiden on me; and thi dredis disturbliden me.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Thei cumpassiden me as watir al dai; thei cumpassiden me togidere.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Thou madist fer fro me a frend and neiybore; and my knowun fro wretchidnesse.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Psalms 88 >