< Psalms 86 >

1 The preier of Dauid. Lord, bowe doun thin eere, and here me; for Y am nedi and pore.
Addu’ar Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, ka kuma amsa mini, gama ni matalauci ne mai bukata kuma.
2 Kepe thou my lijf, for Y am holi; my God, make thou saaf thi seruaunt hopynge in thee.
Ka tsare raina, gama na ba da kaina gare ka. Kai ne Allahna; ka ceci bawanka wanda ya dogara gare ka.
3 Lord, haue thou merci on me, for Y criede al day to thee;
Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, gama na yi kira gare ka dukan yini.
4 make thou glad the soule of thi seruaunt, for whi, Lord, Y haue reisid my soule to thee.
Ka ba bawanka farin ciki gama gare ka, ya Ubangiji, na miƙa raina.
5 For thou, Lord, art swete and mylde; and of myche merci to alle men inwardli clepynge thee.
Kai mai gafartawa da kuma mai alheri ne, ya Ubangiji, cike da ƙauna ga dukan waɗanda suke kira gare ka.
6 Lord, perseyue thou my preier with eeris; and yyue thou tente to the vois of my bisechyng.
Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; ka saurari kukata na neman jinƙai.
7 In the dai of my tribulacioun Y criede to thee; for thou herdist me.
A lokacin wahala zan yi kira gare ka, gama za ka amsa mini.
8 Lord, noon among goddis is lijk thee; and noon is euene to thi werkis.
A cikin alloli babu kamar ka, ya Ubangiji; babu ayyukan da za a kwatanta da naka.
9 Lord, alle folkis, whiche euere thou madist, schulen come, and worschipe bifore thee; and thei schulen glorifie thi name.
Dukan al’umman da ka yi za su zo su yi sujada a gabanka, ya Ubangiji; za su kawo ɗaukaka ga sunanka.
10 For thou art ful greet, and makinge merueils; thou art God aloone.
Gama kai mai girma ne kana kuma aikata ayyuka masu banmamaki; kai kaɗai ne Allah.
11 Lord, lede thou me forth in thi weie, and Y schal entre in thi treuthe; myn herte be glad, that it drede thi name.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji, zan kuwa yi tafiya cikin gaskiyarka; ka ba ni zuciya wadda ba tă rabu ba, don in ji tsoron sunanka.
12 Mi Lord God, Y schal knouleche to thee in al myn herte; and Y schal glorifie thi name withouten ende.
Zan yabe ka, ya Ubangiji Allahna, da dukan zuciyata; zan ɗaukaka sunanka har abada.
13 For thi merci is greet on me; and thou deliueridist my soule fro the lower helle. (Sheol h7585)
Gama ƙaunarka da girma take gare ni; kai ka cece ni daga zurfafa, daga mazaunin matattu. (Sheol h7585)
14 God, wickid men han rise vp on me; and the synagoge of myyti men han souyt my lijf; and thei han not set forth thee in her siyt.
Masu girman kai suna kai mini hari, ya Allah; ƙungiyar marasa imani suna neman raina, mutanen da ba su kula da kai ba.
15 And thou, Lord God, doynge merci, and merciful; pacient, and of myche merci, and sothefast.
Amma kai, ya Ubangiji, kai Allah mai tausayi ne da kuma mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna da aminci.
16 Biholde on me, and haue mercy on me, yyue thou the empire to thi child; and make thou saaf the sone of thin handmayden.
Ka juyo gare ni ka yi mini jinƙai; ka ba wa bawanka ƙarfi; ka ceci ni gama na bauta maka yadda mahaifiyata ta yi.
17 Make thou with me a signe in good, that thei se, that haten me, and be aschamed; for thou, Lord, hast helpid me, and hast coumfortid me.
Ka ba ni alamar alherinka, don abokan gābana su gani su kuma sha kunya, gama kai, ya Ubangiji, ka taimake ni ka kuma ta’azantar da ni.

< Psalms 86 >