< Psalms 82 >

1 Of Asaph. God stood in the synagoge of goddis; forsothe he demeth goddis in the myddil.
Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
2 Hou longe demen ye wickidnesse; and taken the faces of synneris?
“Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
3 Deme ye to the nedi man, and to the modirles child; iustifie ye the meke man and pore.
Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
4 Raueische ye out a pore man; and delyuere ye the nedi man fro the hond of the synner.
Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
5 Thei knewen not, nether vndirstoden, thei goen in derknessis; alle the foundementis of erthe schulen be moued.
“Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
6 I seide, Ye ben goddis; and alle ye ben the sones of hiy God.
“Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
7 But ye schulen die as men; and ye schulen falle doun as oon of the princis.
Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
8 Ryse, thou God, deme thou the erthe; for thou schalt haue eritage in alle folkis.
Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.

< Psalms 82 >