< Psalms 73 >

1 `The salm of Asaph. God of Israel is ful good; to hem that ben of riytful herte.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 But my feet weren moued almeest; my steppis weren sched out almeest.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 For Y louede feruentli on wickid men; seynge the pees of synneris.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 For biholdyng is not to the deth of hem; and stidefastnesse in the sikenesse of hem.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 Thei ben not in the trauel of men; and thei schulen not be betun with men.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Therfore pride helde hem; thei weren hilid with her wickidnesse and vnfeithfulnesse.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 The wickidnesse of hem cam forth as of fatnesse; thei yeden in to desire of herte.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 Thei thouyten and spaken weiwardnesse; thei spaken wickidnesse an hiy.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 Thei puttiden her mouth in to heuene; and her tunge passide in erthe.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Therfor my puple schal be conuertid here; and fulle daies schulen be foundun in hem.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 And thei seiden, How woot God; and whether kunnyng is an heiye, `that is, in heuene?
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Lo! thilke synneris and hauynge aboundance in the world; helden richessis.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 And Y seide, Therfor without cause Y iustifiede myn herte; and waischide myn hoondis among innocentis.
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 And Y was betun al dai; and my chastisyng was in morutidis.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 If Y seide, Y schal telle thus; lo! Y repreuede the nacioun of thi sones.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 I gesside, that Y schulde knowe this; trauel is bifore me.
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 Til Y entre in to the seyntuarie of God; and vndurstonde in the last thingis of hem.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Netheles for gilis thou hast put to hem; thou castidist hem doun, while thei weren reisid.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 Hou ben thei maad into desolacioun; thei failiden sodeynli, thei perischiden for her wickidnesse.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 As the dreem of men that risen; Lord, thou schalt dryue her ymage to nouyt in thi citee.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 For myn herte is enflaumed, and my reynes ben chaungid;
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 and Y am dryuun to nouyt, and Y wiste not.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 As a werk beeste Y am maad at thee; and Y am euere with thee.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 Thou heldist my riythond, and in thi wille thou leddist me forth; and with glorie thou tokist me vp.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 For whi what is to me in heuene; and what wolde Y of thee on erthe?
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 Mi fleische and myn herte failide; God of myn herte, and my part is God withouten ende.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 For lo! thei that drawen awei fer hem silf fro thee, `bi deedli synne, schulen perische; thou hast lost alle men that doen fornycacioun fro thee.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 But it is good to me to cleue to God; and to sette myn hope in the Lord God. That Y telle alle thi prechyngis; in the yatis of the douyter of Syon.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< Psalms 73 >