< Psalms 7 >
1 For the ignoraunce of Dauid, which he songe to the Lord on the wordis of Ethiopien, the sone of Gemyny. Mi Lord God, Y haue hopid in thee; make thou me saaf fro alle that pursuen me, and delyuere thou me.
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 Lest ony tyme he as a lioun rauysche my soule; the while noon is that ayenbieth, nether that makith saaf.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 Mi Lord God, if Y dide this thing, if wickidnesse is in myn hondis;
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 if Y `yeldide to men yeldynge to me yuels, falle Y `bi disseruyng voide fro myn enemyes;
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 myn enemy pursue my soule, and take, and defoule my lijf in erthe; and brynge my glorie in to dust.
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Lord, rise thou vp in thin ire; and be thou reysid in the coostis of myn enemyes.
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 And, my Lord God, rise thou in the comaundement, which thou `hast comaundid; and the synagoge of puplis schal cumpasse thee.
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 And for this go thou ayen an hiy; the Lord demeth puplis. Lord, deme thou me bi my riytfulnesse; and bi myn innocence on me.
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 The wickidnesse of synneris be endid; and thou, God, sekyng the hertis and reynes, schalt dresse a iust man.
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 Mi iust help is of the Lord; that makith saaf riytful men in herte.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 The Lord is a iust iuge, stronge and pacient; whether he is wrooth bi alle daies?
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 If ye ben `not conuertid, he schal florische his swerd; he hath bent his bouwe, and made it redi.
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 And therynne he hath maad redi the vessels of deth; he hath fulli maad his arewis with brennynge thingis.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Lo! he conseyuede sorewe; he peynfuli brouyte forth vnriytfulnesse, and childide wickidnesse.
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 He openide a lake, and diggide it out; and he felde in to the dich which he made.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 His sorewe schal be turned in to his heed; and his wickidnesse schal come doun in to his necke.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 I schal knouleche to the Lord bi his riytfulnesse; and Y schal synge to the name of the hiyeste Lord.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.