< Psalms 69 >

1 `In Ebreu thus, To the victorie, on the roosis of Dauid. `In Jerom thus, To the ouercomer, for the sones of Dauid. God, make thou me saaf; for watris `entriden til to my soule.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
2 I am set in the sliym of the depthe; and `substaunce is not. I cam in to the depthe of the see; and the tempest drenchide me.
Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
3 I traueilide criynge, my cheekis weren maad hoose; myn iyen failiden, the while Y hope in to my God.
Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
4 Thei that hatiden me with out cause; weren multiplied aboue the heeris of myn heed. Myn enemyes that pursueden me vniustli weren coumfortid; Y paiede thanne tho thingis, whiche Y rauischide not.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
5 God, thou knowist myn vnkunnyng; and my trespassis ben not hid fro thee.
Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
6 Lord, Lord of vertues; thei, that abiden thee, be not aschamed in me. God of Israel; thei, that seken thee, be not schent on me.
Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
7 For Y suffride schenschipe for thee; schame hilide my face.
Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
8 I am maad a straunger to my britheren; and a pilgryme to the sones of my modir.
Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
9 For the feruent loue of thin hous eet me; and the schenschipis of men seiynge schenschipis to thee fellen on me.
gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
10 And Y hilide my soule with fastyng; and it was maad in to schenschip to me.
Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
11 And Y puttide my cloth an heire; and Y am maad to hem in to a parable.
sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
12 Thei, that saten in the yate, spaken ayens me; and thei, that drunken wien, sungen of me.
Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
13 But Lord, Y dresse my preier to thee; God, Y abide the tyme of good plesaunce. Here thou me in the multitude of thi mercy; in the treuthe of thin heelthe.
Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
14 Delyuer thou me fro the cley, that Y be not faste set in; delyuere thou me fro hem that haten me, and fro depthe of watris.
Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
15 The tempest of watir drenche not me, nethir the depthe swolowe me; nethir the pit make streit his mouth on me.
Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
16 Lord, here thou me, for thi merci is benygne; vp the multitude of thi merciful doyngis biholde thou in to me.
Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
17 And turne not awei thi face fro thi child; for Y am in tribulacioun, here thou me swiftli.
Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
18 Yyue thou tente to my soule, and delyuer thou it; for myn enemyes delyuere thou me.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
19 Thou knowist my schenschip, and my dispysyng; and my schame.
Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
20 Alle that troblen me ben in thi siyt; myn herte abood schendschipe, and wretchidnesse. And Y abood hym, that was sory togidere, and noon was; and that schulde coumforte, and Y foond not.
Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
21 And thei yauen galle in to my meete; and in my thirst thei yauen `to me drinke with vynegre.
Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
22 The boord of hem be maad bifore hem in to a snare; and in to yeldyngis, and in to sclaundir.
Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
23 Her iyen be maad derk, that thei se not; and euere bouwe doun the bak of hem.
Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
24 Schede out thin ire on hem; and the strong veniaunce of thin ire take hem.
Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
25 The habitacioun of hem be maad forsakun; and `noon be that dwelle in the tabernaclis of hem.
Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
26 For thei pursueden hym, whom thou hast smyte; and thei addiden on the sorewe of my woundis.
Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
27 Adde thou wickidnesse on the wickidnesse of hem; and entre thei not in to thi riytwisnesse.
Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
28 Be thei don awei fro the book of lyuynge men; and be thei not writun with iust men.
Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
29 I am pore and sorewful; God, thin heelthe took me vp.
Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
30 I schal herye the name of God with song; and Y schal magnefye hym in heriyng.
Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
31 And it schal plese God more than a newe calf; bryngynge forth hornes and clees.
Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
32 Pore men se, and be glad; seke ye God, and youre soule schal lyue.
Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
33 For the Lord herde pore men; and dispiside not hise boundun men.
Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
34 Heuenes and erthe, herye hym; the se, and alle crepynge bestis in tho, herye hym.
Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
35 For God schal make saaf Syon; and the citees of Juda schulen be bildid. And thei schulen dwelle there; and thei schulen gete it bi eritage.
gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
36 And the seed of hise seruauntis schal haue it in possessioun; and thei that louen his name, schulen dwelle ther ynne.
’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.

< Psalms 69 >