< Psalms 68 >

1 To the victorie, the salm `of the song `of Dauid. God rise vp, and hise enemyes be scaterid; and thei that haten hym fle fro his face.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
2 As smoke failith, faile thei; as wax fletith fro the face of fier, so perische synneris fro the face of God.
Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
3 And iust men eete, and make fulli ioye in the siyt of God; and delite thei in gladnesse.
Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
4 Synge ye to God, seie ye salm to his name; make ye weie to hym, that stieth on the goyng doun, the Lord is name to hym. Make ye fulli ioye in his siyt, enemyes schulen be disturblid fro the face of hym,
Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
5 which is the fadir of fadirles and modirles children; and the iuge of widewis.
Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
6 God is in his hooli place; God that makith men of o wille to dwelle in the hous. Which leedith out bi strengthe hem that ben boundun; in lijk maner hem that maken scharp, that dwellen in sepulcris.
Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
7 God, whanne thou yedist out in the siyt of thi puple; whanne thou passidist forth in the desert.
Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
8 The erthe was moued, for heuenes droppiden doun fro the face of God of Synay; fro the face of God of Israel.
duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
9 God, thou schalt departe wilful reyn to thin eritage, and it was sijk; but thou madist it parfit.
Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
10 Thi beestis schulen dwelle therynne; God, thou hast maad redi in thi swetnesse to the pore man.
Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
11 The Lord schal yyue a word; to hem that prechen the gospel with myche vertu.
Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
12 The kyngis of vertues ben maad loued of the derlyng; and to the fairnesse of the hous to departe spuylis.
“Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
13 If ye slepen among the myddil of eritagis, the fetheris of the culuer ben of siluer; and the hyndrere thingis of the bak therof ben in the shynyng of gold.
Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
14 While the king of heuene demeth kyngis theronne, thei schulen be maad whitter then snow in Selmon;
Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
15 the hille of God is a fat hille. The cruddid hil is a fat hil;
Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
16 wherto bileuen ye falsli, cruddid hillis? The hil in which it plesith wel God to dwelle ther ynne; for the Lord schal dwelle `in to the ende.
Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
17 The chare of God is manyfoold with ten thousynde, a thousynde of hem that ben glad; the Lord was in hem, in Syna, in the hooli.
Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
18 Thou stiedist an hiy, thou tokist caitiftee; thou resseyuedist yiftis among men. For whi thou tokist hem that bileueden not; for to dwelle in the Lord God.
Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
19 Blessid be the Lord ech dai; the God of oure heelthis schal make an eesie wei to vs.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
20 Oure God is God to make men saaf; and outgoyng fro deeth is of the Lord God.
Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
21 Netheles God schal breke the heedis of hise enemyes; the cop of the heere of hem that goen in her trespassis.
Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
22 The Lord seide, Y schal turne fro Basan; Y schal turne in to the depthe of the see.
Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
23 That thi foot be deppid in blood; the tunge of thi doggis be dippid in blood of the enemyes of hym.
don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
24 God, thei sien thi goyngis yn; the goyngis yn of my God, of my king, which is in the hooli.
Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
25 Prynces ioyned with syngeris camen bifore; in the myddil of yonge dameselis syngynge in tympans.
A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
26 In chirchis blesse ye God; blesse ye the Lord fro the wellis of Israel.
Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
27 There Beniamyn, a yonge man; in the rauyschyng of mynde. The princis of Juda weren the duykis of hem; the princis of Zabulon, the princis of Neptalym.
Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
28 God, comaunde thou to thi vertu; God, conferme thou this thing, which thou hast wrouyt in vs.
Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
29 Fro thi temple, which is in Jerusalem; kyngis schulen offre yiftis to thee.
Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
30 Blame thou the wielde beestis of the reheed, the gaderyng togidere of bolis is among the kien of puplis; that thei exclude hem that ben preuyd bi siluer. Distrie thou folkis that wolen batels,
Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
31 legatis schulen come fro Egipt; Ethiopie schal come bifore the hondis therof to God.
Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
32 Rewmes of the erthe, synge ye to God; seie ye salm to the Lord.
Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
33 Singe ye to God; that stiede on the heuene of heuene at the eest. Lo! he schal yyue to his vois the vois of vertu, yyue ye glorie to God on Israel;
gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
34 his greet doyng and his vertu is in the cloudis.
Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
35 God is wondirful in hise seyntis; God of Israel, he schal yyue vertu, and strengthe to his puple; blessid be God.
Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!

< Psalms 68 >