< Psalms 64 >

1 `In Ebrewe thus, To the victorie, the salm of Dauid. `In Jerom `thus, To the ouercomer, the song of Dauid. God, here thou my preier, whanne Y biseche; delyuere thou my soule fro the drede of the enemy.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
2 Thou hast defendid me fro the couent of yuele doers; fro the multitude of hem that worchen wickidnesse.
Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
3 For thei scharpiden her tungis as a swerd, thei benten a bowe, a bittir thing;
Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
4 for to schete in priuetees hym that is vnwemmed.
Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
5 Sodeynli thei schulen schete hym, and thei schulen not drede; thei maden stidefast to hem silf a wickid word. Thei telden, that thei schulden hide snaris; thei seiden, Who schal se hem?
Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
6 Thei souyten wickidnessis; thei souyten, and failiden in sekinge. A man neiyhe to deep herte;
Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
7 and God schal be enhaunsid. The arowis of `litle men ben maad the woundis of hem;
Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
8 and the tungis of hem ben maad sijk ayens hem. Alle men ben disturblid, that sien hem;
Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
9 and ech man dredde. And thei telden the werkis of God; and vndurstoden the dedis of God.
Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
10 The iust man schal be glad in the Lord, and schal hope in hym; and alle men of riytful herte schulen be preisid.
Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!

< Psalms 64 >