< Psalms 62 >

1 To the victorie on Iditum, the salm of Dauid. Whether my soule schal not be suget to God; for myn heelthe is of hym.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
2 For whi he is bothe my God, and myn heelthe; my `taker vp, Y schal no more be moued.
Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
3 Hou longe fallen ye on a man? alle ye sleen; as to a wal bowid, and a wal of stoon with out morter cast doun.
Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
4 Netheles thei thouyten to putte awei my prijs, Y ran in thirst; with her mouth thei blessiden, and in her herte thei cursiden.
Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
5 Netheles, my soule, be thou suget to God; for my pacience is of hym.
Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 For he is my God, and my saueour; myn helpere, Y schal not passe out.
Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 Myn helthe, and my glorie is in God; God is the yyuer of myn help, and myn hope is in God.
Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 Al the gaderyng togidere of the puple, hope ye in God, schede ye out youre hertis bifore hym; God is oure helpere with outen ende.
Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
9 Netheles the sones of men ben veyne; the sones of men ben liers in balauncis, that thei disseyue of vanytee in to the same thing.
Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
10 Nile ye haue hope in wickidnesse, and nyle ye coueyte raueyns; if ritchessis be plenteuouse, nyle ye sette the herte therto.
Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
11 God spak onys, Y herde these twei thingis, that power is of God, and, thou Lord, mercy is to thee;
Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
12 for thou schalt yelde to ech man bi hise werkis.
kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”

< Psalms 62 >