< Psalms 41 >
1 For victorie, the song of Dauid. Blessid is he that vndurstondith `on a nedi man and pore; the Lord schal delyuere hym in the yuel dai.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Mai albarka ne wanda yake jin tausayin marasa ƙarfi; Ubangiji yakan kuɓutar da shi a lokutan wahala.
2 The Lord kepe hym, and quykene hym, and make hym blesful in the lond; and bitake not hym in to the wille of his enemyes.
Ubangiji zai kāre shi yă kuma kiyaye ransa; zai albarkace shi a cikin ƙasar ba kuwa zai miƙa shi ga hannun maƙiyansa ba.
3 The Lord bere help to hym on the bed of his sorewe; thou hast ofte turned al his bed stre in his sijknesse.
Ubangiji zai ba shi ƙarfi a gadon rashin lafiyarsa ya mayar masa da lafiya daga ciwon da ya kwantar da shi.
4 I seide, Lord, haue thou mercy on me; heele thou my soule, for Y synnede ayens thee.
Na ce, “Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai; ka warkar da ni, gama na yi maka zunubi.”
5 Myn enemyes seiden yuels to me; Whanne schal he die, and his name schal perische?
Abokan gābana suna muguwar magana a kaina cewa, “Yaushe zai mutu sunansa yă ɓace ne?”
6 And if he entride for to se, he spak veyn thingis; his herte gaderide wickidnesse to hym silf.
Duk sa’ad da wani ya zo ganina, yakan yi maganar ƙarya, yayinda zuciyarsa tana tattare da cin zarafi; sa’an nan yă fita yă yi ta bazawa ko’ina.
7 He yede with out forth; and spak to the same thing. Alle myn enemyes bacbitiden pryuyli ayens me; ayens me thei thouyten yuels to me.
Dukan abokan gābana suna raɗa tare a kaina; suna fata mugun abu ya same ni, suna cewa,
8 Thei ordeineden an yuel word ayens me; Whether he that slepith, schal not leie to, that he rise ayen?
“Mugun ciwo ya kama shi; ba zai taɓa tashi daga inda yake kwanciya ba.”
9 For whi the man of my pees, in whom Y hopide, he that eet my looues; made greet disseit on me.
Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
10 But thou, Lord, haue merci on me, and reise me ayen; and Y schal yelde to hem.
Amma kai, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, ka tā da ni, don in sāka musu.
11 In this thing Y knew, that thou woldist me; for myn enemye schal not haue ioye on me.
Na sani kana jin daɗina, gama abokin gābana ba zai ci nasara a kaina ba.
12 Forsothe thou hast take me vp for ynnocence; and hast confermed me in thi siyt with outen ende.
Cikin mutuncina ka riƙe ni ka sa ni a gabanka har abada.
13 Blessid be the Lord God of Israel, fro the world and in to the world; be it doon, be it doon.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, har abada abadin.