< Psalms 30 >

1 The salm of song, for the halewyng of the hows of Dauid. Lord, Y schal enhaunse thee, for thou hast vp take me; and thou delitidist not myn enemyes on me.
Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
2 Mi Lord God, Y criede to thee; and thou madist me hool.
Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
3 Lord, thou leddist out my soule fro helle; thou sauedist me fro hem that goen doun into the lake. (Sheol h7585)
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol h7585)
4 Ye seyntis of the Lord, synge to the Lord; and knowleche ye to the mynde of his hoolynesse.
Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
5 For ire is in his indignacioun; and lijf is in his wille. Wepyng schal dwelle at euentid; and gladnesse at the morewtid.
Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
6 Forsothe Y seide in my plentee; Y schal not be moued with outen ende.
Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
7 Lord, in thi wille; thou hast youe vertu to my fairnesse. Thou turnedist awei thi face fro me; and Y am maad disturblid.
Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
8 Lord, Y schal crye to thee; and Y schal preye to my God.
A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
9 What profit is in my blood; while Y go doun in to corrupcioun? Whether dust schal knouleche to thee; ethir schal telle thi treuthe?
“Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
10 The Lord herde, and hadde merci on me; the Lord is maad myn helpere.
Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
11 Thou hast turned my weilyng in to ioye to me; thou hast to-rent my sak, and hast cumpassid me with gladnesse.
Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
12 That my glorie synge to thee, and Y be not compunct; my Lord God, Y schal knouleche to thee with outen ende.
don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.

< Psalms 30 >