< Psalms 12 >

1 To the victorie on the eiyte, the song of Dauid. Lord, make thou me saaf, for the hooli failide; for treuthis ben maad litle fro the sones of men.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi. Bisa ga sheminit. Zabura ta Dawuda. Ka taimaka, Ubangiji, gama masu tsoron Allah ba sa nan kuma; masu aminci sun ɓace daga cikin mutane.
2 Thei spaken veyn thingis, ech man to hys neiybore; thei han gileful lippis, thei spaken in herte and herte.
Kowa yana yi wa maƙwabcinsa ƙarya; zaƙin bakinsu maganar ƙarya ce suna cike da ruɗu a zukatansu.
3 The Lord destrie alle gileful lippis; and the greet spekynge tunge.
Bari Ubangiji yă yanke dukan zaƙin bakinsu da kuma kowane harshe mai fariya,
4 Whiche seiden, We schulen magnyfie oure tunge, our lippis ben of vs; who is oure lord?
masu cewa, “Da harsunanmu za mu yi nasara; leɓunanmu za su kāre mu, wane ne maigidanmu?”
5 For the wretchednesse of nedy men, and for the weilyng of pore men; now Y schal ryse vp, seith the Lord. I schal sette inhelt he; Y schal do tristili in hym.
“Saboda danniyar marasa ƙarfi da kuma nishin masu bukata, zan tashi yanzu,” in ji Ubangiji. “Zan kāre su daga masu yin musu sharri.”
6 The spechis of the Lord ben chast spechis; siluer examynyd bi fier, preued fro erthe, purgid seuen fold.
Kalmomin Ubangiji kuwa ba su da kuskure, kamar azurfan da aka tace cikin matoyan yumɓu, aka tsabtacce sau bakwai.
7 Thou, Lord, schalt kepe vs; and thou `schalt kepe vs fro this generacioun with outen ende.
Ya Ubangiji, za ka kiyaye mu lafiya ka tsare mu daga irin mutanen nan har abada.
8 Wickid men goen in cumpas; bi thin hiynesse thou hast multiplied the sones of men.
Mugaye suna yawo a sake sa’ad da ake girmama abin da ba shi da kyau a cikin mutane.

< Psalms 12 >