< Psalms 102 >
1 The preier of a pore man, whanne he was angwishid, and schedde out his speche bifore the Lord. Lord, here thou my preier; and my crie come to thee.
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Turne not awei thi face fro me; in what euere dai Y am troblid, bowe doun thin eere to me. In what euere day Y schal inwardli clepe thee; here thou me swiftli.
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 For my daies han failid as smoke; and my boonus han dried vp as critouns.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 I am smytun as hei, and myn herte dried vp; for Y haue foryete to eete my breed.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Of the vois of my weilyng; my boon cleuede to my fleische.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 I am maad lijk a pellican of wildirnesse; Y am maad as a niyt crowe in an hous.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 I wakide; and Y am maad as a solitarie sparowe in the roof.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Al dai myn enemyes dispisiden me; and thei that preisiden me sworen ayens me.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 For Y eet aschis as breed; and Y meddlide my drinke with weping.
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 Fro the face of the ire of thin indignacioun; for thou reisinge me hast hurtlid me doun.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Mi daies boweden awei as a schadewe; and Y wexede drie as hei.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 But, Lord, thou dwellist with outen ende; and thi memorial in generacioun and in to generacioun.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Lord, thou risinge vp schalt haue merci on Sion; for the tyme `to haue merci therof cometh, for the tyme cometh.
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 For the stones therof plesiden thi seruauntis; and thei schulen haue merci on the lond therof.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 And, Lord, hethen men schulen drede thi name; and alle kingis of erthe schulen drede thi glori.
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 For the Lord hath bildid Sion; and he schal be seen in his glorie.
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 He bihelde on the preier of meke men; and he dispiside not the preier of hem.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Be these thingis writun in an othere generacioun; and the puple that schal be maad schal preise the Lord.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 For he bihelde fro his hiye hooli place; the Lord lokide fro heuene in to erthe.
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 For to here the weilingis of feterid men; and for to vnbynde the sones of slayn men.
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 That thei telle in Sion the name of the Lord; and his preising in Jerusalem.
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 In gaderinge togidere puplis in to oon; and kingis, that thei serue the Lord.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 It answeride to hym in the weie of his vertu; Telle thou to me the fewnesse of my daies.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Ayenclepe thou not me in the myddil of my daies; thi yeris ben in generacioun and in to generacioun.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 Lord, thou foundidist the erthe in the bigynnyng; and heuenes ben the werkis of thin hondis.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Tho schulen perische, but thou dwellist perfitli; and alle schulen wexe eelde as a clooth. And thou schalt chaunge hem as an hiling, and tho schulen be chaungid;
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 but thou art the same thi silf, and thi yeeris schulen not faile.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 The sones of thi seruauntis schulen dwelle; and the seed of hem schal be dressid in to the world.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”